• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Abin da ya sa za a naɗa ni Kogunan Ɗanja ranar Asabar mai zuwa – Ashiru Bazanga

by DAGA ABBA MUHAMMAD
June 13, 2022
in Labarai
0
Katin gayyatar zuwa naɗin Ashiru Sani Bazanga

Katin gayyatar zuwa naɗin Ashiru Sani Bazanga

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN jarumi kuma furodusa,  Malam Ashiru Sani Bazanga (Sawun Keke), ya bayyana farin ciki kan bikin naɗa shi sarautar Kogunan Ɗanja da za a yi a ranar Asabar mai zuwa, 18 ga Yuni, 2022, a fadar Sarkin Kudun Katsina da ke garin Ɗanja a Jihar Katsina.

Sarkin Kudun Katsina, Hakimin Ɗanja da ke Ƙaramar Hukumar Ɗanja, Alhaji M.T. Bature, shi ne zai naɗa shi tare da wasu manyan mutane da misalin ƙarfe 10:00 na safe.A hirar sa da mujallar Fim, Bazanga ya ce tarayyar sa da Sarkin Kudu ɗin ce ta sa aka ba shi wannan sarauta, ba nema ya yi ba.

Ya ce, “Domin shi da karan kan shi tunanin shi ya ba shi, bayan ya shekara 30 a kan karagar mulki ba tare da duk waɗannan naɗe-naɗen ba, sai  dagatan sa waɗanda su ke kusa da shi su ka matsa masa da ya yi ƙoƙari ya yi irin wannan naɗin. Sai Allah bai sa hankalin sa ya yi wajen ba, kuma da ya zo ya yarda zai yi bikin cika shekara talatin a kan gadon mulki, wanda a ranar 4 ga Yuni, 2022 ya cika shekara talatin ɗin cur.

“Saboda abin ya zo a takure da batutuwan zaɓuɓɓukan ‘yan siyasa, shi kuma waɗanda ya yi tunanin ya naɗa duk ‘yan siyasa ne, wannan ya sa ya ɗage bikin zuwa ranar da za a yi wannan naɗi. 

“Amma tsakani da Allah, ni tarayya ce da mutunci da girma da girmamawa ta sa aka ba ni sarautar, ba don na nema ba.”

Dangane da yadda ya ji a ran sa a kan wannan sarauta da za a yi masa, Bazanga ya ce, “Alhamdu lillahi, sai in ce ina godiya ga Ubangiji. Ina kuma godiya ga iyaye da su ka sa mu a hanyoyin da su ka zama na girma, na mutunci, na daraja, har Allah ya sanya mu ke tare da manyan mutane. 

“Kuma ina miƙa godiya da jinjinar ban-girma ga shi mai girma Sarkin Kudun Katsina, Hakimin Ɗanja, Alhaji M.T. Bature Ibrahim Nadabo.”

Ya ƙara da cewa, “Kuma ina yi Allah godiya da ya ba mu dama mu ka kawo wannan lokacin, bayan ina Ɗanmasanin Nassarawan Kaduna, wanda mai girma Sarkin Nassarawa Abubakar Adamu ya naɗa ni, kuma yau ga shi Allah ya kai mu a ƙasa ta, mahaifa ta, hakimi na, kuma hakimin farko, Sarkin Kudun farko a Jihar Katsina, Alhaji M.T. Bature, ya ba ni wannan sarauta ta  Kogunan Katsina. 

“Babu abin da zan ce in ban da godiya tare da addu’a, da fatan Allah ya zaunar da ƙasar mu lafiya, ya kuma albarkaci masarautar mai girma Alhaji M.T. Bature da kuma masarautar mai martaba Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman.” 

Da ya ke tsokaci kan masu sukar ‘yan fim da maganganu marasa daɗi, sai kuma ga shi ana ɗaukar su ɗaya bayan ɗaya ana ba su sarauta, sabon Kogunan ya kada baki ya ce, “Ka ga amsa ta zo a bakin ka, tunda ga shi har ana ɗauko ɗaiɗaikun mu ana naɗawa. Ka ga kenan shi kuma shi mai kalma a kan mutum, in ya ɓata ya sani, in ya gyara ya sani. Kuma duk wanda ka ga ya na zagin wani mutum ko waɗansu al’umma, waɗanda su ba su san su na yi ba, sakayya ta na wurin Ubangiji. 

“Ai an yi wannan a Jihar Kano. An samu wani wanda ya zo a gwamnati ya takura wa duk  masu wannan sana’ar, ya ci mutuncin mutane  fiye da tunanin al’umma. A ƙarshe ya zo Kaduna don ya ci zarafin mu, ni kai na saboda baƙin cikin wannan abin da ya yi, ban san shi ba, bai san ni ba, amma na ji wai har da ni ya ke zagi ya na ci mana mutunci, na ji ba zan yarda ba, har aiki na bari saboda wannan mutumin. 

“To ka ga kenan mu na da mutunci, mu na da daraja. Kuma alhamdu lillahi, sarakuna da manyan malamai sun san mu, sun san darajar mu, sun san mutuncin mu, kuma su na girmama mu. 

“Ga shi nan a yanzu haka a cikin mu akwai hakimai da dama. Akwai waɗanda sarakuna ne yanzu, su ma kan su ‘yan wasan kwaikwayo ne. Misali, Sarkin Maskan Katsina, ya na cikin ‘Samanja Mazan Fama’, ai daga nan wasan kwaikwayo ya fara ko? Ka dubi ƙasar Zazzau irin su Tafarkin Zazzau, mai girma Jafaru ko? Hakimi ne yanzu. Ga su nan in za mu yi lissafi su na da yawa. 

“Akwai manyan malamai ma waɗanda mu ka taso tun mu na yara yanzu sun zama wata tsiya a ƙasar nan, kuma duk mun yi wasan da su. 

“Shugabanci ba irin wanda ‘yan fim ba su yi. Sai dai ban ƙi maka ba da ake cewa wake ɗaya shi ke ɓata gari. Idan a cikin mu akwai baragurbi, Allah ya shirya su, ya sa su fahimta, kuma su daina ɓata mana suna. 

“Amma masu yi mana kuɗin goro ɗin nan, kuskure ne. Ni yanzu ka ga ni ai rabon da in shiga wasan kwaikwayo ban san iyakar kwanakin ba, ban san iyakar watannin ba. Amma duk inda na ji an zagi ɗan wasan kwaikwayo ko ɗan fim, sai in ji kamar an soke ni da mashi a zuciya don ka kashe ni, domin na san ba ka faɗi gaskiya ba, kuma na san ka ci mutunci, kuma na san ka zalunce mu, kuma za mu bar ka da fitowar rana da faɗuwar ta.”

Shi dai Ashiru Sani Bazanga, ɗan jarida ne a gidan rediyo da talbijin na Liberty da ke Abuja, amma ya taɓa yin aiki a gidan rediyo da talbijin na Alheri da DITV a Kaduna da Rediyon Jihar Kaduna da Rediyon Tarayyar Nijeriya na Kaduna da Muryar Nijeriya a Legas a lokuta daban-daban.

Ya yi fice ne musamman a wasan kwaikwayo na talbijin mai suna ‘Sawun Keke’ wanda aka riƙa nunawa a gidan talbijin na Jihar Kaduna a shekarun baya, sannan da harkar finafinan bidiyo ta zo kuma ya shirya finafinai da su ka haɗa da ‘Aminan Zamani’.

Loading

Tags: Ɗanmasanin Nassarawa KadunaHakimin ƊanjaLiberty RaedioM.T. BaturesarautaSarkin Katsina Abdulmimini Kabir UsmanSarkin Kudun KatsinaSarkin Nassarawa Abubakar Adamu
Previous Post

In da ran ka…!

Next Post

‘Soyayyar Facebook’: Hadiza Gabon ta faɗa wa alƙali: Ban san mai iƙirarin neman aure na ba

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Hadiza Aliyu Gabon

'Soyayyar Facebook': Hadiza Gabon ta faɗa wa alƙali: Ban san mai iƙirarin neman aure na ba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!