• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

An kasafta sama da N5m don ceto rayuwar Magajiya Ɗambatta

by DAGA IRO MAMMAN
December 30, 2019
in Labarai
0
Hajiya Magajiya Ɗambatta a gidan ta a Makoɗa jiya

Hajiya Magajiya Ɗambatta a gidan ta a Makoɗa jiya

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

WANI kwamiti da fitaccen ɗan jarida Jaafar Jaafar ya kafa ya yi kasafin zunzurutun kuɗi har naira miliyan biyar domin inganta rayuwar shahararriyar zabiyar nan Magajiya Ɗambatta.

 Idan kun tuna, mujallar Fim ta ba ku labarin yadda Jaafar ya gano zabiyar a garin Makoɗa cikin Jihar Kano, ta na rayuwa cikin ƙunci, har da bara domin samun abinci.

 Jaafar da wasu aminan sa sun kafa gidauniya don tara kuɗin da za su yi amfani da su wajen ceto rayuwar zabiyar mai waƙar ‘Soriyal’ daga halin ƙaƙa-ni-ka-yi.

 Ya zuwa lokacin da mu ka ba labarin a makon jiya, jama’ar Annabi da su ka ga bayanan Jaafar sun tara kuɗin agaji sama da N400,000.

 To ya zuwa jiya kuma kuɗin sun kai har naira miliyan biyar da dubu shida da ɗari biyu da ashirin da biyu (N5,006,222).

 Jaafar ya bayyana cewa mutane 576 ne su ka bada gudunmawar wannan kuɗin.

 Mujallar Fim ta ga cewa a jerin sunayen waɗanda su ka bada gudunmawar akwai wanda ya bada har rabin miliyan, to akwai kuma wanda ya bada N200 kacal.

Jaafar (a tsaye a hagu) tare da ‘yan kwamiti da jikokin Magajiya

Jaafar ya ce a yanzu dai an rufe karɓar taimakon, ya na mai farin ciki da cewa abin da aka tara ya zarce tunanin ‘yan kwamitin nasu.

 Haka kuma ya bayyana cewa sun ziyarci Magajiya Ɗambatta a Makoɗa jiya, inda shi da sauran ‘yan kwamitin (Musa Sufi, Ibrahim Sanyi-Sanyi, da Munzali Hausawa) su ka labarta mata abin da aka tara da kuma nufin su game da wannan kuɗi.

 Magajiya ta yi godiya ga duk wanda ya taimaka ya bada wannan agaji gare ta.

 Wani likita, Dakta Kabir Abdussalam, ya binciki lafiyar mawaƙiyar, kuma ya bada shawarar cewa za a kai ta asibiti a sake duba lafiyar idon ta, da fatan ko za a yi dace a magance mata makantar da ta yi.

 Jaafar ya ce sun jima a garin su na bincike tare da tattaunawa da ‘yan’uwan ta da maƙwabtan ta da dattijan garin kan abin da ya dace a yi.

 ‘Yan kwamitin sun sa wani dillali a garin ya nemo filin sayarwa inda za a gina mata gida ko kuma idan an samu gidan sayarwar ma ana so.

 An ware kuɗi masu dama domin a gina mata gida ko kuma a sayi ginanne.

 Jaafar ya sanar da cewa an kasafta kuɗi domin kula da Hajiya Magajiya Ɗambatta a tsawon shekara uku masu zuwa.

 Kasafin, wanda mujallar Fim ta gani, shi ne:

 1. Kuɗin kashewa a duk wata: N15,000. Za a riƙa ba ta N5,000 a kowane kwana 10. Kuma ita za a ba kuɗin kai-tsaye. Jimilla a shekara ɗaya shi ne N180,000.

 2. A duk bayan wata huɗu za a ba ta N15,000 kuɗin sayen sabulu, man shafawa, turare da sauran su. N5,000 za a riƙa ba ta a duk wata. Jimilla a shekara ɗaya shi ne N60,000.  

3. Za a ba ta N40,000 kuɗin kayan Sallah a duk shekara, wato N20,000 a kowane bikin Sallah kenan.

 4. N12,000 kuɗin abincin rana da na dare a kowane wata. N200 sau 2, wanda ya kama N400 sau kwana talatin. Za a bada waɗannan kuɗi ga wasu jikokin ta biyu maza masu aure waɗanda su za su riƙa ciyar da ita. An shawarta cewa idan wannan jika ya ciyar da ita tsawon wata ɗaya, sai ɗayan ya amsa, shi ma wata ɗaya. An yi haka ne don a samu sauƙi da tabbatar da komai ya tafi daidai. Jimillar wannan kuɗi a shekara shi ne N144,000.

 5. Za a riƙa ba wata jikanyar ta alawus ɗin N5,000 a duk wata domin kula da tsaftar ta. Wannan yarinya ita ce mai share mata ɗaki kuma ta wanke mata sutura. Jimilla a shekara shi ne N60,000.

 6. Za a ba yarinyar nan ‘yar jagorar Magajiya N3,000 na zuwa makaranta a duk wata. Wato ya kama N100 a kowace rana, sau kwana 30. Za a damƙa kuɗin a hannun uwar ita ‘yar jagorar. Jimilla a shekara shi ne N36,000. 

Jadawalin kuɗaɗen da ‘yan kwamiti su ka kashe a ziyarar da su ka kai jiya

Jimillar dukkan waɗannan kuɗaɗe a shekara ɗaya shi ne N520,000.  

Jimillar waɗannan kuɗaɗe da za a kashe a shekara 3 shi ne N1,560,000. 

Agajin farko: Ana saukar da kayan abinci da su Jaafar su ka kawo wa Magajiya

Mujallar Fim ta fahimci cewa da yake jimillar kuɗin sun kai miliyan biyar, za a cire waɗannan miliyan ɗaya da rabi da ‘yan kai, sannan a cire kuɗin sayen gida ko gina gida daga ciki (bakin abin da ya kama), daga nan kuma abin da ya rage za a aje shi saboda gaba. 

Jaafar ya bayyana cewa ko ƙwandala kwamitin su ya kashe kan wannan hidima, to zai yi bayani a kan ta, duk duniya ta gani.

Dandazon ‘yan kallo lokacin da ‘yan kwamitin agajin Magajiya Ɗambatta su ka isa garin Makoɗa

 A kafafen soshiyal midiya dai ana ci gaba da yi wa su Jaafar ruwan yabo da addu’ar Allah ya biya su ladar wannan namijin ƙoƙari da su ka yi na ceto rayuwar Magajiya Ɗambatta daga halin ƙunci da ta shiga. 

Loading

Previous Post

Zamfara ta nemi agajin Kano kan aikin tace fim

Next Post

Masana sun zaburar da matasa kan sanin harshen Ingilishi

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Dama zuwa hagu: Farfesa Munzali Jibril, Farfesa Abdalla Uba Adamu da Dakta Bala Muhammad

Masana sun zaburar da matasa kan sanin harshen Ingilishi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!