• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

An maka mawaƙi Rarara a kotu kan kuɗi sama da naira miliyan goma

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
April 8, 2023
in Labarai
0
Dauda Rarara

Dauda Rarara

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

AN gurfanar da shahararren mawaƙi Dauda Adamu Abdullahi Kahutu (Rarara) a gaban babbar kotun shari’ar Musulunci da ke unguwar Rijiyar Zaki a Kano kan kuɗi naira miliyan goma da dubu ɗari uku (N10.3m).

Wata majiya ta shaida wa mujallar Fim cewa wani mutum mai suna Muhammad Ma’aji ne ya yi ƙarar mawaƙin kan waɗannan kuɗaɗe da ya ke bin sa. 

Ma’aji ya shaida wa kotu cewa akwai wata harka su ka ƙulla shi da Rarara a watannin baya, amma yanzu ba shi da wani zaɓi don ya karɓi haƙƙin sa sai ta fannin shari’a.

Ya ce ya bi matakin sulhu da Rarara don ya ba shi kuɗin sa tunda dai harkar da su ka kulla ba ta yiwu ba, amma mawaƙin ya ƙi biyan shi.

Kakakin manyan kotunan Shari’ar Musulunci na Jihar Kano, Malam Muzammil Ado Fagge, ya bayyana yadda Rarara ya dinga wasan ɓoyo da masinjan kotu don kada a ba shi sammaci. 

Ya ce: “Wannan ƙara ce wadda Muhammad Ma’aji ya shigar da Rarara, kuma ƙara ce wadda akwai mu’amulla da shi har ta naira miliyan 10 kuma ya yi ya yi ya bashi ƙuɗin amma ya ƙi.

 “Don haka mun yi amfani da doka da oda ta 9, 2021 da ta yi magana cewa idan aka nemi mutum don a ba shi sammaci ba a gan shi ba to za a iya yin amfani da shafukan sada zumunta don sanar da shi ko kuma a liƙa masa a gidan sa.

“Shi wannan mawaƙin sai wasan ɓuya ya ke yi da jami’in mu don ya ba shi sammacin amma ya ƙi yarda su haɗu, shi ya sa mu ka nemi mai unguwar sa da kuma shaidu mu ka liƙa masa a gidan sa da ke Zoo Road, domin tabbatar da bin doka wajen isar masa da saƙon kotun.”

Malam Muzammil ya ce za a fara sauraren ƙarar a ranar Talata mai zuwa, 11 ga Afrilu, 2023 a kotun wadda Mai Shari’a Halhaltul Khuza’i Zakariya ke jagoranta.

Loading

Tags: Dauda Abdullahi Kahutu RararakotuMuhammad Ma'ajiMuzammil Ado FaggeShari'ar Musulunci
Previous Post

Ya kamata ‘yan fim mu ɗauki darasin watan Ramadan, inji A’isha Tafida Gombe

Next Post

Mawaƙi Lilin Baba ya ba hadimin sa, Murtala Bloko kyautar mota

Related Posts

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry
Labarai

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry

June 15, 2025
Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
Next Post
Hotunan da Murtala Bloko ya haɗa a Instagram, inda ake ganin sa tare da Lilin Baba da motar da ya ba shi

Mawaƙi Lilin Baba ya ba hadimin sa, Murtala Bloko kyautar mota

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!