• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Bikin Fadila Kurfi: Katsina za ta ɗau kwambar marubuta

by DAGA IRO MAMMAN
December 25, 2019
in Ranar Murna
0
Fadila H. Aliyu Kurfi

Fadila H. Aliyu Kurfi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
ANA sa ran cewa birnin Katsina zai cika da manyan marubutan littattafan Hausa a ranar Alhamis da Juma’a mai zuwa, 26 da 27 ga Disamba, 2019, saboda bikin auren ‘yar’uwar su da za a yi, wato Hajiya Fadila H. Aliyu Kurfi.

Fadila za ta auri wani wanda aka faɗa wa mujallar Fim cewa ya na daga cikin manyan hadiman Gwamna Aminu Bello Masari na Jihar Katsina ne a fagen siyasa mai suna Hon. Tanimu Sada Sa’ad.

A katin gayyatar zuwa ɗaurin auren da aka raba, an nuna cewa za a ɗaura auren fitacciyar marubuciyar ne a garin su, wato Kurfi, Jihar Katsina, a ranar Juma’a, 27 ga wata.

Wakilin mu ya samu labarin cewa ɗaya daga cikin abubuwan ban-sha’awa da ake shiryawa a bikin shi ne gasar rubuta gajerun labarai da waƙoƙi waɗanda za a gabatar a lokacin taron bikin.

Za a yi taron a Katsina a ranar Alhamis.

A ranar Juma’a kuma ɗaurin aure, wanda da zaran an gama shi, shi kenan an sallami kowa.

Tun daga lokacin da labarin auren ya ɓulla, kamar wata ɗaya da ya gabata, marubuta daga wasu jihohin su ke ta shirin tafiya Katsina inda za su haɗu da marubutan da ke jihar, a ci bikin tare da su.

Mujallar Fim ta ji yadda marubuta daga Kano da Kaduna da wasu garuruwan su ke ta bayyana ƙudirin su na halartar wannan biki.

Shugabar ɗaya daga cikin manyan ƙungiyoyin marubuta da ake da su, wato Ƙungiyar Marubuta ta Alƙalam da ke Kaduna, Hajiya Halima K/Mashi, ta faɗa wa wakilin mu cewa, “Abin da ya sa ka ga mu na ta ɗokin zuwa bikin Fadila shi ne saboda ita Fadila ba ta yin sanyi-sanyi da duk wata hidima ta marubuta.

“In dai an saka ta a wani sha’ani na marubuta, to sai inda ƙarfin ta ya ƙare; shi ya sa mu ma za mu je domin taya ta murna.”

Ta yi nuni da yadda Fadila ta jajirce wajen tabbatar da nasarar Taron Duniya na marubutan Hausa da aka yi har karo biyu, ɗaya a Kano ɗayan a Kaduna, ta ce lallai Fadila ta cancanci a taya murna da kuma addu’a.

Wata majiya ta shaida wa mujallar Fim cewa tuni kwamitin tsare-tsaren bikin ya shirya wa manyan baƙi abinci da wurin kwana.

Wata majiyar kuma ta kurkusa da Fadilar ta faɗa wa mujallar Fim cewa amaryar za ta tare ne a Kano inda mijin ya ke da gida.

Majiyar ta ƙara da cewa Fadila za ta kasance matar Tanimu ta biyu, domin ya na da uwargidan sa a cikin Katsina.

Wannan shi ne aure na biyu da marubuciyar za ta yi. Auren ta na fari ya mutu ne a ‘yan shekarun baya bayan sun samu ‘ya guda ɗaya mai suna Ibtihal.

To Allah ya sa alheri, ya ba su zaman lafiya, amin.

Loading

Previous Post

Kabiru Jammaje zai gabatar da sabon littafin koyon Turanci

Next Post

Su Jaafar Jaafar sun fara tara kuɗi domin agaza wa zabiya Magajiya Ɗambatta

Related Posts

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
An ɗaura auren darakta a Kannywood, Al-Amin Ciroma da ‘yar’uwar sa Sharifatu
Ranar Murna

An ɗaura auren darakta a Kannywood, Al-Amin Ciroma da ‘yar’uwar sa Sharifatu

May 2, 2025
Ƙarshen tika-tika, tik! A’ishatulhumaira ta zama matar Rarara ta huɗu
Ranar Murna

Ƙarshen tika-tika, tik! A’ishatulhumaira ta zama matar Rarara ta huɗu

April 25, 2025
Darakta Al-Amin Ciroma zai yi amarya a watan gobe, shekaru biyu bayan mutuwar auren sa da Wasila Isma’il 
Ranar Murna

Darakta Al-Amin Ciroma zai yi amarya a watan gobe, shekaru biyu bayan mutuwar auren sa da Wasila Isma’il 

April 20, 2025
Ahlan tare da 'yar sa Hassana, amaryar mako mai zuwa
Ranar Murna

Jarumi a Kannywood, Ahlan zai aurar da ‘yar sa Hassana

February 16, 2025
Daɗi kan daɗi: Marubuciya Bilkisu Yusuf Ali ta samu jika da digirin digirgir
Ranar Murna

Daɗi kan daɗi: Marubuciya Bilkisu Yusuf Ali ta samu jika da digirin digirgir

December 20, 2024
Next Post
Magajiya Ɗambatta da 'yar jagora za su fita yawon bara. Hoto daga Jaafar Jaafar

Su Jaafar Jaafar sun fara tara kuɗi domin agaza wa zabiya Magajiya Ɗambatta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!