• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cewar Hadiza Gabon a kotu: Rayuwa ta ta na cikin haɗari

by DAGA IRO MAMMAN
August 1, 2022
in Labarai
0
Hadiza Aliyu Gabon

Hadiza Aliyu Gabon

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCIYAR jarumar Kannywood Hadiza Gabon ta bayyana cewa shari’ar da ake tafkawa da ita a Kaduna ta jefa rayuwar ta cikin haɗari.

Ta faɗi haka ne a gaban alƙalin kotun Shari’ar Musulunci da ke Magajin Gari, Kaduna, a yau Litinin a cigaba da sauraren ƙarar ta da wani mutum ya kai ta.

Idan kun tuna, mujallar Fim ta ba ku labarin yadda wani ma’aikacin gwamnati mai suna Bala Musa ya maka ta a kotun bisa zargin cewa ta ci masa kuɗi har N396,000 sannan ta ƙi auren sa.

Jarumar, wadda ke zama a Kaduna, ta faɗa wa kotun a zaman da aka yi a baya cewa wannan magana dai zuƙi ta malle ce, domin ita ba ta ma san mutumin ba.

Alƙalin ya ɗage sauraron ƙarar daga ranar 28 ga Yuni, 2022, zuwa yau, 1 ga Agusta, saboda rashin lafiyar matar sa.

A yau ne aka ba Musa damar ya kawo shaidun da ya ce ya na da su.

Sai dai Hadiza Gabon ta shaida wa kotun, ta bakin lauyan ta, Barista Mubarak Sani Jibril, cewa taɓarɓarewar tsaro a ƙasar nan ya sa jarumar ta na jin tsoron zuwa kotun.

Ya ce jarumar ta na tsoron yadda a duk ranar da aka dawo kotu domin cigaba da sauraron ƙarar sai an yi dabarar ficewa da ita daga kotun.

Lauyan ya ce: “Tsaron lafiya ta ya na da muhimmanci, ita ma tsaron lafiyar ta ya na da muhimmanci, sannan tsaron lafiyar sauran jama’a ma ya na da muhimmanci a kotun, har ma da shi mai ƙarar.

“Rayuwa ta ta na cikin haɗari, rayuwar ta ta na cikin haɗari, rayuwar shi ma mai ƙarar ta na cikin haɗari. Ba mu san waye ke bibiyar shari’ar a soshiyal midiya ba. Abu na gaba shi ne za ka fara ganin ‘yan bindiga a nan sun zo satar mutane domin garkuwa da su. Wannan shi ne abin da ya dame mu, ba shari’ar da ake yi a kotu ba.”

Lauyan ya yi kira ga alƙalin da ya yi la’akari da tsaron lafiyar wadda ake ƙara ya ba ta damar ta daina zuwa kotun domin cigaba da sauraron ƙarar.

Da jin haka, sai lauyan mai ƙara, wato Barista Naira Murtala, ya ƙi amincewa da wannan roƙon, ya ce tilas ne wadda ake ƙarar ta zo kotu a ko yaushe.

A kan batun tsaron lafiyar wadda ake ƙarar kuwa, ya ce ba zai ƙi amincewa da roƙon da su ka yi ba saboda da gaske ne babu tsaro ga kowa a ƙasar, to amma akwai buƙatar su kawo shi a rubuce domin ya duba ya yi nazari.

Alƙalin kotun, Khadi Rilwanu Kyaudai, ya ba su tabbacin cewa kotun za ta duba batun tsaron lafiyar masu shari’ar a zaman kotun na gaba.

Loading

Tags: Bala MusaBarista Mubarak Sani JibrilBarista Naira MurtalaHadiza GabonKhadiKhadi Rilwanu KyaudailauyaMagajin Garirashin tsaroshari'a.
Previous Post

Gidan yanar kallon finafinan Hausa, Kallo.ng, ya samu karramawa ta duniya

Next Post

Mun sauya ofis ne saboda kiyaye mutuncin Kannywood – Alhasan Kwalle

Related Posts

AFMAN ta taya Sarari murnar samun damar halartar taron baje-kolin finafinan Nijeriya a Toronto da fim ɗin ‘Kakanda’
Labarai

AFMAN ta taya Sarari murnar samun damar halartar taron baje-kolin finafinan Nijeriya a Toronto da fim ɗin ‘Kakanda’

June 16, 2025
Naɗa ni jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry Powder da aka yi zai amfani Kannywood baki ɗaya, inji furodusa Abubakar Galadima
Labarai

Naɗa ni jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry Powder da aka yi zai amfani Kannywood baki ɗaya, inji furodusa Abubakar Galadima

June 15, 2025
Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
Next Post
Malam Alhassan Kwalle

Mun sauya ofis ne saboda kiyaye mutuncin Kannywood - Alhasan Kwalle

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!