• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Doka ce ta cire Sunusi Oscar442 daga fim ɗi na ba Afakallah ba – Alhaji Sheshe

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
July 30, 2021
in Labarai
0
Doka ce ta cire Sunusi Oscar442 daga fim ɗi na ba Afakallah ba – Alhaji Sheshe
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN furodusa a masana’antar shirya finafinan Hausa ta Kannywood, Mustapha Ahmad, wanda aka fi sani da Alhaji Sheshe, ya musanta zargin da darakta Sunusi Oscar442 ya yi na cewa Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta tilasta maye sunan sa da na wani daraktan a wani fim saboda saɓanin da ke tsakanin sa da shugaban hukumar.

Idan kun tuna, a ranar Litinin da ta gabata, 25 ga Yuli, 2021, mujallar Fim ta wallafa hirar ta ta farko da Oscar442 inda ya zargi shugaban hukumar, Alhaji Isma’il Na’abba (Afakallah), da ɗaukar wasu matakai na musguna masa saboda bambancin siyasa da ke tsakanin su.

Oscar442 ɗan jam’iyyar PDP ne, yayin da Afakallah ya ke aiki a gwamnatin da APC ta kafa.

Oscar442 ya faɗa wa mujallar Fim cewa:  “Ina da matsala da shugaban Hukumar Tace Finafinai. Ba ya ƙauna ta gaba ɗaya, don haka ba wani abu da zan iya yi don in rayu a masana’antar Kannywood in dai ya na nan. Sau da yawa zan yi fim, zai ce in dai ni ne ba zai duba fim ɗin ba. A satin nan ma akwai wani fim ɗi na da na yi, na kamfanin Sheshe, ya ce a cire suna na, in dai ni ne fim ɗin ba zai fita a cikin Jihar Kano ba. To mai kamfanin ya sa aka kira ni, ya ce ga abin da Hukumar Tace Finafinai ta gaya masa. Na ce masa ya yi haƙuri a cire, ba wani abu ba ne ba. Haka aka cire, aka maye suna na da na Ali Gumzak a cikin wannan fim ɗin.”

To amma shi a nasa ɓangaren, Alhaji Sheshe cewa ya yi rashin bin doka ne ya sa aka cire sunan daraktan tun kafin su kai wa hukuma fim ɗin domin tacewa, ba wai Afakallah ne ya sa aka cire sunan ba.

A zantawar sa da mujallar Fim a ofishin sa da ke Kano, Alhaji Sheshe ya kawo wasu dalilai waɗanda ya ce su ne su ka jawo aka cire sunan daraktan daga cikin fim ɗin mai suna ‘Juwairiyya’, wanda aka ɗauka tsawon lokaci kafin ya fito.

Ya ce, “Na wayi gari da ganin labari a kan cewa Hukumar Tace Finafinai ta cire sunan darakta Sunusi Oscar442 kan cewar in dai da sunan sa to ba za ta duba fim ɗi na ba. To, maganar gaskiya Hukumar Tace Finafinai ba ita ce ta sa na cire Oscar daga fim ɗin ‘Juwairiyya’ ba.

“Abin da ya faru shi ne fim ɗin ya kai kusan shekara uku da ɗauka kafin Hukumar Tace Finafinai ta sa dokar cewa duk wani ɗan fim a Kano sai ya yi rijista da ita. A lokacin mu ka ɗauki fim ɗin sai kuma aka samu tsaiko wajen fitowar sa tun a lokacin kafin a sa dokar kenan, sai kuma yanzu mu ke so mu saki fim ɗin. 

“Duba da tsarin Hukumar Tace Finafinai na duk fim ɗin da a yanzu idan akwai wani wanda ba shi da rijista da ita ba za ta duba ba, shi ne ya sa mu ka ɗauki gaɓarar sanar da duk wanda ya san ba shi da  rijista a cikin mutanen da mu ka ɗauki fim ɗin da su da su yi haƙuri za mu cire sunan su za mu sa na waɗanda su ke da rijista.”

Ya ƙara da cewa, “Mu na so za mu fitar da fim ɗin mu a kasuwa, yanzu kuma ga shi akwai sunan sa a ciki kuma ba shi da rijista da Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano. Hakan ya sa na sa aboki na, Sani Kandi, ya kira wo Sunusi Oscar a waya su ka yi magana ta fahimtar juna, ya kuma gane cewa matsalar daga gare shi ne na rashin yin rijista da hukuma.

“Lokacin da abin ya faru, na ba shi shawarar ya je ya yi rijista tun lokacin da aka fara yin rijista ta farko. Na ce masa shi darakta ne, ya kamata ya zo ya yi rijista saboda a ci gaba da sana’a tare.

Alhaji Sheshe tare da Ismail Na’abba (Afakallah)

“Sai ya nuna min shi ba zai yi rijista ba wani mutum ya sa shi a aljihu, shi harkokin sa ya fi yi a Abuja, wato waƙe-waƙe ne, don haka ba shi da buƙatar yin rijista a Jihar Kano daga nan zuwa shekara biyu ko uku ma nan gaba. 

“To, duba da haka ya sa na nemi izinin sa kan cewa na cire sunan sa saboda zan kai fim ɗi na a duba min don ina so na saki fim ɗin a kasuwa. A nan ya amince, ya mana fatan alkairi. Na cire sunan sa.”

Alhaji Sheshe ya ce, “Ana cikin wannan abu, kwatsam! sai na ga ya yi hira a kan cewa Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta ce ba za ta duba fim ɗin ba in dai da sunan sa a ciki. Ni kuma ba mu yi haka da Hukumar Tace Finafinai ba.

“Kai, hasali ma ba ta san waye daraktan fim ɗi na ba, kawai dai na san cewa idan na kai fim ɗi na da sunan daraktan da ba shi da rijista da hukumar, to ba za ta duba ba.

“Ina tabbatar da cewa shi kan sa fim ɗin ba a kai shi wurin Hukumar Tace Finafinai da sunan sa ba, ballantana su ce ba za su duba ba. 

“Kuma mun yi finafinai guda biyu da Oscar, ɗaya mai suna ‘Ƙazamin Shiri’ da kuma wannan ‘Juwairiyya’, wanda a lokacin da ‘Ƙazamin Shiri’ ya fita babu doka ta cewar sai ka na da rijista kuma na kai hukuma ta duba fim ɗin.

“Kuma a lokacin ya na jam’iyyar PDP, kuma da man shi bai taɓa fita daga ita ba, ni ma kuma ɗan PDP ne, mu na ma da ‘yar tsama tsakanin mu da APC a lokacin, amma na kai fim ɗin aka duba min aka ban shaida wato satifiket, na haska shi a sinima. Yanzu ga shi ana sa shi ma a tashar Arewa24.”

Alhaji Sheshe ya jaddada cewa babu wata alaƙar siyasa da ta sa aka cire sunan Oscar442 daga wannan fim ɗin domin kuwa ya ce idan da alaƙar siyasa ce, to da shi ma an cire sunan sa don shi ma ɗan PDP ne, kowa ya sani, kuma duk abin da wani mutum ya ke ji ya ba wa PDP gudunmawa da rayuwar sa ko da jikin sa shi ma ya ce ya bayar in dai a masana’antar fim ne.

“Irin gudunmawar da mu ka ba wa PDP ba lallai wasu daga cikin masu tafiyar PDP sun bayar ba,” inji shi.

Babban furodusan ya yi kira ga abokan sana’ar sa da su yi ƙoƙari su riƙa bin dokar gwamnati domin a cewar sa ita gwamnati ba a ja da ita, ikon Allah ce.

Ya ce: “Ka bi dokar ta ka zauna lafiya, ka ƙi bin dokar ta ka shiga ruɗani. Wannan kira ne ga abokai na na sana’a da kuma na cikin jam’iyya ta ta PDP da su ke harkar fim.”

Alhaji Sheshe a wurin wani taro

Loading

Tags: Alhaji ShesheCensorship in Nigeriahausa filmsHukumar Tace Finafinai ta Jihar KanoKannywoodKano State Censorship BoardSunusi Oscar442
Previous Post

MOPPAN za ta agaza wa Rahama A. Ibrahim, sabuwar jaruma da ta musulunta

Next Post

Burin Platinum Cinema shi ne ta haɓaka Kannywood – Babatunde Adeniji

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Burin Platinum Cinema shi ne ta haɓaka Kannywood – Babatunde Adeniji

Burin Platinum Cinema shi ne ta haɓaka Kannywood - Babatunde Adeniji

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!