• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Furodusan Kannywood Umar UK ya yi ƙarar Hafsat Idris ya na so ta biya shi diyyar naira miliyan 10

by DAGA IRO MAMMAN
October 7, 2021
in Labarai
0
Hafsat Idris da Umar UK

Hafsat Idris da Umar UK

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

UMAR UK, ɗaya daga cikin manyan furodusoshin Kannywood, ya maka fitacciyar jaruma Hafsat Idris (Ɓarauniya) a kotu, ya na neman diyya kan ƙin zuwa ɗaukar wani shirin sa na talbijin da ta yi bayan ya biya kuɗi har naira miliyan ɗaya da dubu ɗari uku (N1,300,000).

Umar, mai kamfanin UK Entertainment, ya na neman diyyar naira miliyan 10 daga jarumar a bisa tuhumar karya yarjejeniya.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa furodusan ya shigar da ƙarar ne Babbar Kotun Kano ta 14 da ke yankin Ƙaramar Hukumar Ungogo cikin birnin Kano.

A cikin takardar ƙarar da wakilin mu ya gani, Umar ya yi iƙirarin cewa ya biya Hafsat kuɗin ne domin ta fito masa a wani shirin takbijin mai suna ‘Girke-Girken Afrika’ da ya ke shiryawa. An fara ɗaukar shirin da ita, amma kwatsam sai ta yi ƙemadagas ta daina zuwa.

A cewar sa, hakan da ta yi ya saɓa wa alƙawarin da su ka yi a rubuce.

Umar ya faɗa wa kotun, a ƙarƙashin Mai Shari’a Ibrahim Abdullah, cewa ya samu asara mai yawa sakamakon daina zuwa shirin da Hafsat ta yi.

Saboda haka ya buƙaci kotun da ta umarce ta ta biya shi diyyar naira miliyan 10, kuma ta dawo masa da shigar cinikin da ya ba ta.

A ranar da aka zauna a kotun dai Hafsat ba ta je ba, amma ta shigar da tata kariyar a rubuce a kotun ta hanyar lauyan ta.

Daga nan alƙalin ya ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 19 ga Oktoba, 2021.

Alƙali Ibrahim ya bada umarnin a sake kai wa jarumar sammaci domin ta halarci kotun a ranar da za a koma.

Mujallar Fim ta samu labarin cewa Umar UK ya yi yarjejeniya da wani gidan talbijin ɗin satalayit da ke ƙasar Ghana mai suna ‘Gaskiya TV’ ne domin su riƙa nuna shirin girke-girken, kamar yadda tashar talbijin ta ‘African Magic’ ke haska shirin “Girke-Girken Hauwa Maina”.

Sakamakon rugujewar harkar kasuwancin finafinan Kannywood, furodusoshi da dama sun faɗaɗa tunanin su wajen shirya wasu shirye-shirye da za a kalla, musamman ta hanyar talbijin, sinima ko YouTube.

Binciken mujallar Fim ya nuna cewa tun da fari, naira miliyan biyu Hafsat ta buƙaci Umar ya biya ta, amma bayan roƙon ta da ya yi sai ta yi masa ragin ɗari bakwai.

A yarjejeniyar aikin, an amince cewar idan za a fita aikin za a sanar da ita a kan lokaci, sannan idan ta na da uziri za a iya ɗagawa.

A cewar majiyar mu, an yi nisa da aikin, rannan sai aka sanar da jarumar cewa gobe za a fita zuwa aikin, amma ita kuma ta na Kaduna, don haka ta buƙaci a ɗaga ranar.

“To da yake sau biyu kenan ana ɗagawa, sai Umar ya ji haushi, ya ƙi ɗaga ranar. Sai ya maye gurbin Hafsat da Jamila Nagudu, kuma ya cire Hafsat daga shirin,” inji mai ba mu labarin.

Sakamakon haka rai a ɓaci a ɓangarorin biyu, inda a ƙarshe Umar ya nemi jarumar da ta dawo masa da kuɗin sa.

Majiyar mu ta ce ganin halin da ake ciki sai fitaccen furodusan nan, Tahir Elkinana, ya kira Umar da Hafsat taron sasantawa a ofishin sa.

Da aka zo taron, sai Umar ya zo da takardar ƙarar Hafsat, ya miƙa wa Elkinana, wanda jami’in gwamnatin jihar ne. “Haka kuma a daren sai ya saka labarin a gidan rediyo, aka yayata,” inji majiyar mu.

Yaɗa labarin a rediyo ya ɓata wa Hafsat rai, har ta yi niyyar za ta kai Umar kotu a kan ya ɓata mata suna idan an gama shari’ar su.

Da ranar zuwa kotu ta zo, aka fara sauraren ƙarar.

Loading

Tags: African MagicGaskiya TVHafsat Idrishausa filmsJamila NaguduJustice Ibrahim AbdullahKannywoodKano State High CourtTahir ElkinanaUK EntertainmentUmar UK
Previous Post

Cewar Al-Amin Ciroma: Na yi mamaki da hamdala da mu ka cika shekara 19 da aure da Wasila Isma’il

Next Post

Zabiya Magajiya Ɗambatta ta rasu ta na da shekara 85

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Marigayiya Magajiya Ɗambatta a ɗakin ta cikin sabon gidan da su Jaafar su ka gina mata. Hoto daga: Daily Nigerian

Zabiya Magajiya Ɗambatta ta rasu ta na da shekara 85

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!