• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnati na aiki tuƙuru kan karɓo sauran ‘yan matan Chibok – Minista Sadiya

by DAGA WAKILIN MU
April 15, 2021
in Nijeriya
0
Gwamnati na aiki tuƙuru kan karɓo sauran ‘yan matan Chibok – Minista Sadiya
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAR Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta na ci gaba da aiki ba tare da gajiyawa ba domin ta ceto sauran ‘yan matan Chibok waɗanda aka sace shekaru bakwai da su ka gabata.

Ministar ta yi wannan maganar ne a ranar Laraba lokacin da ta ke jimamin abin baƙin cikin nan da ya faru na satar ɗaruruwan ‘yan matan daga makarantar su ta kwana da ke garin Chibok a Jihar Borno.

Mayaƙan Boko Haram ne su ka sace ‘yan matan.

Sadiya Farouq ta ce ta na matuƙar alhinin abin da ya faru kuma ta yi addu’ar Allah ya sada sauran ‘yan matan da aka sace da iyalan su nan ba da daɗewa ba.

Ta ce, “A matsayi na na Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, ina jin zafin a ce an cika shekaru bakwai tun da aka sace ‘yan matan Chibok. 

Ɗaya daga cikin iyayen ‘yan matan Chibok na alhinin cika shekara bakwai tun da aka sace mata ‘ya

“Gwamnatin mu ta samu mulki ne bisa hurumin jama’a na kawo ƙarshen ta’addanci a yankin Arewa-maso-gabas wanda shi ne ya janyo sace ‘yan matan na Chibok kuma ta yaƙi cin hancin da ya hana a yi aikin ceto su.

“Mun samu nasara sosai, to amma har yanzu akwai sauran aiki ga dukkan matakan gwamnati. An ceto rabin yawan ‘yan matan an sada su da iyalan su kuma sun ci gaba da makaranta. Za mu ci gaba da aiki domin mu dawo da sauran waɗanda su ka rage.”

Ministar ta yi la’akari da cewa gwamnatoci a matakan ƙaramar hukuma, jiha da kuma tarayya sun inganta abin da su ke yi idan an kai hare-hare a makarantu kuma su na aiki bakin ƙarfin su don hana kai hare-haren.

“Ba zan iya bayyana irin dabarun tsaro da matakan da ake ɗauka a fili ba, amma ina tabbatar maku da cewa gwamnati ta ɗauki tsaron lafiyar jama’ar ta a matsayin muhimmin aiki. Mu na yaƙar ambaliyar ayyukan laifi ne da zazzafan tsattsauran ra’ayi a yankin tare da haɗin gwiwar wasu.  

“Bari in kwantar wa da iyayen yarinyar Chibok ɗin nan, Leah Sharibu, da na sauran waɗanda aka kama cewar wannan gwamnatin ba ta manta da ku ba. Mun ji buƙatun ku, kuma ma’aikatu da hukumomin da abin ya shafa za su yi wani abu a madadin gwamnati.

“Dukkan ‘ya’yan mu sun cancanci a ba su ilimi. Ƙasar mu na buƙatar a ilimantar da su don ci-gaban mu. Babu wanda za a ce ya zaɓi ko dai makaranta ko zaman lafiya.

“Za mu yi dukkan abin da ya kamata don mu ba kowane yaro ɗan Nijeriya damar ficewa daga ƙangin fatara kuma ya cimma burin rayuwar sa.”

A ranar 14 ga Afrilu, 2014 ne dai ‘yan ta’adda su ka kama ‘yan mata 276 a cikin dare a Makarantar Sakandare ta Chibok, su ka gudu da su.

Previous Post

Cewar Zee-Zee: Abin da ya sa aka ce na mutu

Next Post

Rarara ya bada tallafin miliyan 3 ga ‘yan fim 60 saboda azumin Ramadan

Related Posts

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Next Post
Rarara: Fim ɗi na, ‘Gidan Dambe’, zai agaza wa ‘yan wasan Ibro

Rarara ya bada tallafin miliyan 3 ga 'yan fim 60 saboda azumin Ramadan

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!