• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Haramcin fim kan kidinafin da daba: Ba zan iya faɗa da gwamnati ba – Asase

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
September 24, 2021
in Labarai
1
Tijjani Asase

Tijjani Asase

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A CI-gaba da martanin da furodusoshi da daraktocin Kannywood ke yi game da haramcin da Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta yi wa finafinai masu nuna kidinafin, shaye-shaye da ƙwacen waya, fitaccen jarumi Tijjani Abdullahi (Asase) ya ce shi idan aka ce ya daina shirya fim ɗin sa mai dogon zango na ‘A Duniya’, to zai daina, domin shi ba zai iya faɗa da gwamnati ba.

Ya ce: “An ce faɗan da ya fi ƙarfin ka sai ka maida shi wasa.”

Idan kun tuna, shugaban hukumar, Alhaji Isma’il Na’abba (Afakallah), ya faɗa wa mujallar Fim a ranar Talatar nan cewa sun ɗauki wannan matakin ne domin kare mutunci da al’adar mutanen Kano.

Asase na ɗaya daga cikin furodusoshin da ake ganin dokar za ta shafa saboda fim ɗin sa mai suna ‘A Duniya’, wanda ke hasko yadda wasu matasa ke yin harkar daba a Kano.

Duk da haka, jarumin kuma furodusa ya ce abin da ya kamata su Afallah su yi shi ne su yi koyi da Hukumar Tace Finafinai ta Ƙasa, wadda ta bayyana cewa duk mutumin da ya yi laifi a cikin fim, to a nuna sakamakon aikata laifin da ya yi, kada a ba shi mutunci ko girmamawa.

Game da jigon fim ɗin sa, Asase ya faɗa wa mujallar Fim cewa, “Ba wai ina yin fim ɗi na ‘A Duniya’ don shaye-shaye ko daba ba, a’a, akwai wasu ɗabi’u da Allah ya ɗaukaka su a fim ɗin da ɗaukaka darajar fim ɗin, shi ya sa ido ya yi yawa a kan fim ɗin, ake kallon fim ɗin haka.

“Akwai finafinan da ake yin su a kan daba da waye-waye.

Sanarwar soma haska ‘A Duniya a tashar Africa Magic

“Ni finafinai na ina da saƙo da na ke so na isar kuma ina isar da su a hankali, ina kaiwa ga inda na ke tunani a lissafi na zan kai. 

“Kuma a ko da yaushe ina maimaitawa idan aka zo da cewar nan abu kaza bai dace ba, nan abu kaza bai dace ba, zan gyara saboda ba ni da sana’ar da ta wuce ta.

“Idan kuma aka ce ba a so gaba ɗaya, to shi ma zan haƙura. An ce faɗan da ya fi ƙarfin ka sai ka maida shi wasa. 

“Ni ba zan yi rigima da gwamnati ba, kuma ba zan ce ban yarda da abin da gwamnati ta ce ba, a’a, face dai ita rayuwar wanda ya yi daidai ya san ya yi daidai, wanda ma bai yi ba ya san ba daidai ya ke aikatawa ba.”

Asase ya ƙara da cewa shi a ko da yaushe kalma ɗaya ce a bakin sa, wato: “Allah ya ba ni ikon yin daidai, kuma Allah ya fahimtar da ni gaskiya, ya kuma ba ni ikon gyarawa. 

“Kuma duk mutumin da ya ke magana a kan gyara, gyara, to ni ko da yaushe kamar raƙumi da akala na ke: idan an ja ni a kan gyara, ina tafiya. Allah ya sa hakan da aka yi shi ne mafi alheri a gare ni. Idan ina ɗauko wani nauyi na zunubi aka sauke min, to shi wannan abin taimaka ta ya yi a rayuwa.”

A game da rol ɗin da ta ke takawa a fim, Asase ya yi batanin cewa, “Ni ba hali na ba ne fitowa a ɗan iska, ba hali na ba ne fitowa a ɗan daba, ba hali na ba ne fitowa a mutumin banza, amma fim wannan rol ɗin ya fi ƙarfi a yadda na ke aiwatarwa a cikin fim ɗin.

“Kuma ni mai son gyara ne a ko da yaushe. Ba na goyon bayan ɓarna. 

“Kuma shi shugaban Hukumar Tace Finafinai ya faɗa ya ce an yi wannan abin ne don al’umma, don mutanen Jihar Kano. To mu ma mu na yin fim ɗin ne don al’umma, don mutanen Jihar Kano. Idan dai ba a yin haka ba daidai ba ne, to in Allah ya yarda ba za mu yi ba, kuma za mu bi doka don duk wanda ya bi doka shi ne zaman lafiya.”

Duk da haka, jarumin ya yi da cewa ya kamata kafin a ɗau wannan matakin a ce an jira su an zauna da su an tattauna.

Ya ce, “Kamata ya yi a ce kafin a yanke hukuncin, tunda mulki ne na siyasa, sai a kirawo mu a ce, ‘To ga matsalolin da ba ma so, ga kuma yadda mu ke so a dinga yi, ga yadda ya dace a zama; idan ka ga za ka iya yi sai ka ci gaba da yi, idan kuma ba za ka iya ba sai ka haƙura’. 

“Amma kuma kamar ina ganin ba komai ba ne, misali ka fito ka ce dole sai an yi shawara da kai idan za a yi wani hukunci tunda ni ba dokar ƙasa na sani ba, ban san yadda dokar ta ke ba, don haka ba zan ce ya zama wajibi dole sai an kira mu ba kafin a yanke hukunci ba. Zan iya tabbatar da hakan daidai ne ko ba haka ba ne? 

Fostar shirin ‘A Duniya’ wanda ake nuna shi a YouTube

“Kawai dai shi wanda ya yi ya san hakan shi ne daidai. Kuma in ba a yi wasa ba, ba shi kaɗai ya yanke ba, kamar ya yi shawara ne ko kuma a gwamnatance ko majalisa ce ta zauna ta zartas da shi ta saka shi a cikin doka tunda ita dokar da ta ke riƙe da hukumar ai majalisa ce ta yi dokar, don haka ka ga shi ma za a ba shi dokar ya karanta ne, kuma ba sai an yi shawara da mu ba.”

Shi dai Asase, likkafar sa ta yi gaba, domin fim kuwa za a fara nuna ɗin sa mai dogon zango na ‘A Duniya’ a tashar talbijin ta Africa Magic Hausa da ke kan satalayit ɗin DSTV da na GoTV daga ranar 1 ga Oktoba, 2021.

Copyright © Fim Magazine. All rights reserved.
www.fimmagazine.com

Loading

Tags: A DuniyaCensorship in Nigeriadrug abusegwamnatihausa filmsHukumar Tace Finafinai ta Jihar KanoKannywoodKanoKano State Censorship BoardkidinafinKidnappingNFVCBshaye-shayeTijjani Asase
Previous Post

Ɗaliban jami’a ‘yan Nijeriya sun karrama Rahama Sadau a Indiya

Next Post

Cewar Adam A. Zango: Matasa mu riƙa kai zuciya nesa

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Adam A. Zango tare da 'yan jarida a lokacin firimiyar 'Ribar Duniya'

Cewar Adam A. Zango: Matasa mu riƙa kai zuciya nesa

Comments 1

  1. Pingback: Bazan Iya Fada Da Gwamnati ba A Shirye Nake Na Daina Fim din A Duniya - Tijjani Assase – HausaLoaded.Com

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!