• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

INEC ta ƙara inganci, masu maguɗi ba za su ci kasuwa a ranar zaɓe ba, inji shugaban Kiristoci

by DAGA WAKILIN MU
March 15, 2022
in Nijeriya
0
Rabaran Fada Polycarp Lubo

Rabaran Fada Polycarp Lubo

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHUGABAN Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN), reshen Jihar Filato, Rabaran Fada Polycarp Lubo, ya yaba wa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), inda ya ce a yanzu hukumar ta inganta, kuma ta kamo hanyar zama sahihiya abin dogaro wajen gudanar da zaɓe karɓaɓɓe.

Da ya ke jawabi wurin wani taron mabiya ɗariƙar Katoliƙa na Pankshin da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Kanke, Lubo ya ce yanzu dai INEC ta inganta, kuma maguɗi ya ragu sosai a wurin zaɓe.

Da ya ke jawabi wurin taron mai taken “Hanyoyin Dacen Samun Gwamnati Tagari, Zaman Lafiya da Ci Gaban Ƙasa”, ya yi kira ga Kiristoci cewa kowa ya tashi ya mallaki katin rajistar zaɓe, domin a zaɓi mutane nagari a kan mulki.

Ya zaburar da Kiristoci su tashi su mallaki katin zaɓe, don huce takaicin su wajen zaɓen shugabanni nagari.

Shugaban ƙungiyar ya jaddada wa Kiristoci cewa hanya ɗaya da a yanzu za su samu shugabanni nagari, ita ce su tashi su mallaki katin zaɓe, domin zaɓen nagari a kan muƙamai daban-daban.

Rabaran Lubo ya ce, “Mallakar katin zaɓe ne kaɗai hanyar da Kiristoci za su bi domin su zaɓi shugabannin ƙwarai kuma nagari.

“Yanzu Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta ƙara gyaruwa, ta kuma ƙara inganci. Irin yawan maguɗin zaɓen da aka riƙa yi a baya, yanzu duk ya ragu sosai.

“Sannan kuma samuwar wannan sabuwar Dokar Zaɓe da aka sa wa hannu zai ƙara canja abubuwa da dama.

“Saboda haka ƙuri’un ku su ne makaman ku, kuma su ne ƙarfin ku na samun shugabanni nagari.

“A da ne ake cewa ƙuri’a ba ta da wani tasiri. Amma a yanzu dai ƙuri’a ce ke da tasiri, ba maguɗi ba.”

Rabaran Lubo ya kuma yi wa Kiristocin da ke kan muƙamai daban-daban na mulki cewa su ji tsoron Ubangiji, su yi gaskiya da kuma riƙe amanar da aka ba su.

Loading

Tags: CANChristiansINECPlateauRev. Fr Polycarp Lubo
Previous Post

Minista Sadiya ta ƙaddamar da shirin bai wa matasan N-Power sama da 460,000 tallafin aikin gona

Next Post

Mawaƙi a Kannywood Albashir Hamza Yareema ya zama angon Sadiya

Related Posts

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Next Post
Ango Albashir da amarya Sadiya

Mawaƙi a Kannywood Albashir Hamza Yareema ya zama angon Sadiya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!