• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

INEC ta fara horas da shugabannin harkar zaɓe kan yawaita rumfuna

by DAGA WAKILIN MU
April 17, 2021
in Nijeriya
0
INEC ta fara horas da shugabannin harkar zaɓe kan yawaita rumfuna
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe Mai Zaman Kan ta ta Ƙasa (INEC) ta fara aikin horas da jami’an ta da ke shugabantar harkar zaɓe a jihohi 36 da Gundumar Birnin Tarayya a kan hanyoyin yawaita rumfunan zaɓe.

Babban Kwamishina a hukumar, Farfesa Okechukwu Ibeanu, shi ne ya bayyana haka a ranar Juma’a a wajen taron bitar kwana biyu da aka shirya wa jami’an a Abuja.

Ya ce an shirya taron bitar ne domin a ƙara wa jami’an ilimi kan ƙoƙarin da ake yi na mayar da ƙananan wuraren kaɗa ƙuri’a (voting points) zuwa rumfunan zaɓe a dukkan faɗin ƙasar nan.

Ibeanu, wanda shi ne shugaban Kwamitin Ayyukan Gudanar da Zaɓe a hukumar, ya ce taron bitar ya na da muhimmanci wajen aiwatar da hanyoyin da za a bi a faɗaɗa rawar da masu jefa ƙuri’a za su taka a harkokin zaɓe a nan gaba.

Ya ƙara da cewa horaswar wani muhimmin aiki ne wajen cimma manufar wata tafiya wadda aka fara ta watanni kaɗan da su ka gabata.

Ya bayyana cewa akwai buƙatu a rubuce har 10,092 da aka kai wa hukumar na samar da rumfunan zaɓe a faɗin ƙasar nan.

Ya ce, “Damar samar da rumfunan zaɓe ga masu zaɓe ya na ta raguwa kuma ƙoƙarin da ake yi na yawaita su bai samu nasara ba saboda hukumar ba ta yi aiki da dabarar da ta dace ba a kan hakan.

“Don haka ake yin sabon ƙoƙarin fara tuntuɓa tare da aiki da masu ruwa da tsaki a faɗin ƙasar nan domin su amince a warware matsalar wadda ta shafi tsarin zaɓen a shekaru 25 da su ka gabata.”

Ibeanu ya ce a wajen yin hakan an fito da shawara to amma akwai buƙatar a aiwatar da shawarar domin a cimma muradi.

“Don a tabbatar da an bi shawarar a yadda ta ke, tilas ne a samar da isasshen horo ga jami’an da ke gudanar da zaɓe waɗanda su ne shugabannin harkar zaɓe a dukkan jihohin, waɗanda su ne za su aiwatarwar da shirin.

“Burin taron bitar shi ne ya tabbatar da cewa an ilmantar da su kan hanyoyin da ake so a bi wajen gudanar da aikin.”

Ibeanu ya ƙara da cewa ana sa ran shugabannin aikin za su maimaita horaswar a jihohin su ga jami’an da ke yankunan ƙananan hukumomi.

Ya ce ana so a kammala aikin horaswar kafin a fara aikin yi wa masu zaɓe rajista a ranar 28 ga Yuni.

Ibeanu ya ce INEC ta na aiki domin ta magance matsalolin da ke kawo cikas ga shigar masu zaɓe cikin tsarin zaɓe kafin a yi manyan zaɓuɓɓuka na ƙasa.

Shi ma a nasa jawabin, Babban Kwamishina na INEC kuma Shugaban Kwamitin Wayar Da Kan Masu Zaɓe da Yaɗa Labarai, Mista Festus Okoye, ya ce samar da rumfunan zaɓe zai samar da damarmaki masu yawa ga sababbin masu yin rajista ta yadda za su samu rumfunan zaɓe cikin sauƙi.

Okoye ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa INEC za ta ci gaba da tuntuɓar Majalisar Tarayya domin a gaggauta aikin yi wa Dokar Zaɓe garambawul.

A cewar sa, wannan zai sa a shigar da sababbin tsare-tsare da za su inganta shigar da masu zaɓe cikin tsarin a ƙasar nan.

Previous Post

Wa ke son ganin bayan Pantami?

Next Post

Za a ƙaddamar da littafin ‘Diwanin Waƙoƙin Aminu Ala’ bayan Sallah

Related Posts

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Next Post
Za a ƙaddamar da littafin ‘Diwanin Waƙoƙin Aminu Ala’ bayan Sallah

Za a ƙaddamar da littafin 'Diwanin Waƙoƙin Aminu Ala' bayan Sallah

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!