• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Littafin ‘Ɗaukar Fansa’: Kwalliya ta biya kuɗin sabulu

by DAGA SANI AHMAD GIWA
March 8, 2020
in Marubuta
0
Aysha Asas riƙe da kambin karramawar ta. A dama, littafin 'Ɗaukar Fansa'

Aysha Asas riƙe da kambin karramawar ta. A dama, littafin 'Ɗaukar Fansa'

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
AN samu nasara a taron baje-kolin littafin ‘Ɗaukar Fansa’ na Aysha Asas wanda ƙungiyar marubuta ta Mikiya ta shirya domin ‘ya’yan ƙungiya da makaranta littattafan Hausa da ƙungiyoyi da manyan mutane da sauran hukumomi da ma’aikatun gwamnatin da ƙungiyar ta ke hulɗa da su, su zo su sayi littafin da ƙarin naira ɗari a kan farashin shi na kasuwa.
 
An ƙaddamar da littafin a Kaduna a ranar 7 ga Maris, 2019.
 
Alhamdu lillahi, kwalliya ta biya kuɗin sabulu! Mikiya ta fito da sabon tsari fil da zai taimaki marubuci a daidai lokacin da kasuwar littafi ta shiga irin wani surƙuƙi.
 
Wannan hanya ta yi tasiri sosai wajen yin kasuwancin littafin, domin tun lokacin da aka yi sanarwar mutanen da su ka aiko da kuɗin su ta asusun banki daga jihohi da garuruwa mabanbanta tabbas su na da yawa, musamman ma mutanen Sokoto da Adamawa. 
 
Kamfanin ‘A.S. Creative Writing & Translation Agency’ kawai sun shaida mana an tura masu da kuɗin kwafen littafi 123 wanda kuɗin su ya kama N51,500. Sai kuma waɗanda aka tura ta asusun banki na mawallafiyar, wato ‘yan’uwa da abokan arziki su ka yi mata kara, su ka tura mata da kuɗin kwafe 130 amma kwafe guda-guda su ke buƙata, inda kuɗin ya kama N65,000 daidai.
 
√ Jinjinar ban-girma ga JRTV da babban daraktan gidan talbijin da rediyon ya sayi kwafe 40 N20,000 amma kwafe biyu ya amsa. Bugu da ƙari ya saya wa ma’aikatan sa da ya zo da su aiki wurin kwafe ashirin, N10,000  amma su ka amshi kwafe biyar.
 
√ Sai kuma Masarautar Zazzau da su ka sayi kwafe ɗari a kan N50,000. Chiroman Shantalin Zazzau ne ya wakilci masarautar.
 
√ Aminiyar mawallafiya, wato Aunty Sadiya Kaduna, ta sayi kwafe a kan N10,000 amma kwafe ɗaya ta ce ta ke buƙata.
 
√ Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, ƙarƙashin jagorancin mai girma Kwamishina Dakta Usman Muhammad Maƙarfi, sun turo da kuɗin kwafe ɗari ta asusun banki N50,000. Sai kuma ofishin PRO waɗanda abokan hulɗar mu ne sosai su ma sun turo da kuɗin kwafe goma sha biyar (N7,500) a daidai lokacin da ake gudanar da baje-kolin littafin.
 
Aysha Asas tare da aminiyar ta, marubuciya Aunty Sadiya Kaduna
√ Ƙungiyar ‘Mikiya Hausa Writers’ ta sayi kwafe 35 da za ta ajiye a ɗakin karatun ta, wanda ya kama N17,500, bayan kuma kowannen ɗan ƙungiya ya sayi adadin kwafe na ƙashin-kai.
 
 
Marubuciyar tare da wasu daga cikin mahalartan taron
√ Hukumar Kula da Ingancin Karatu da Makarantu na Jihar Kaduna, wanda wakilin su ya yi sharhin littafin, sun sayi kwafe 40 a kan N20,000 a ƙarƙashin jagorancin babbar daraktar ma’aikatar, Hajiya Umma K. Ahmad, tare da yi mana wani albishir mai daɗi.
 
√ Godiya da jinjina mai tarin yawa ga mai girma Hakimin Kurmin Mashi bisa ga shawarwarin sa. Haƙiƙa sun zauna a zukatan mu.
 
√ Kai, har zan rufe ban faɗi adadin kwafen da kamfanin ‘Mudassir & Brothers’ su ka saya ba bayan mun tashi daga taron. Sun turo da kuɗin kwafe 70 (N35,000)  domin rarraba wa ma’aikatan su. 
 
√ Ba za mu manta da kamfanin ‘A.S. Creative Writing & Translation Agency’ ba, wanda shi ne ya ɗauki nauyin Gasar Auna Fahimta a kan littafin, amma duk da haka sun sayi kwafe ɗari da hamsin (N75,000).
 
√ Mu na yi wa ƙungiyoyin da su ka halarci taron baje-kolin, musamman Majalisar Gobe Da Labari na gidan DITV/Alheri Radio, Kaduna, godiya, da kuma sauran makaranta da marubuta da su ka zo domin sayen littafin. Haƙiƙa kun nuna mana karamci kuma kwalliya ta biya kuɗin sabulu har da na turaren fesawa.
 
Littafin ‘Ɗaukar Fansa’ ya shiga rukunin littattafan Hausa da su ka shiga kasuwa cikin nasara.
 
Ƙungiyar ‘Mikiya Hausa Writers’ ta fito da sabon salon da zai taimaka sosai don farfaɗo da kasuwancin littafi. Jinjina a gare ku kafatanin ‘ya’yan ƙungiyar Mikiya!
 
Allah ya shige mana gaba.

Loading

Previous Post

Ɗaliban Arewa sun karrama Rarara

Next Post

Ɓarayi sun sace marubuci kuma furodusa Abdullahi Maizare

Related Posts

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 
Marubuta

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 

January 1, 2025
Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 31, 2024
‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 20, 2024
Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai

November 30, 2024
Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau
Marubuta

Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau

November 27, 2024
Ƙungiyar matasa da mata za ta naɗa Ado Gidan Dabino Sarkin Mawallafan Arewa
Marubuta

Gasar rubutu: Hukumar Tace Finafinai ta bayyana gwaraza 50 na zagayen farko

November 24, 2024
Next Post
Malam Abdullahi Yahaya Maizare

Ɓarayi sun sace marubuci kuma furodusa Abdullahi Maizare

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!