• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, May 18, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Marubuci Maizare ya kuɓuta daga hannun ɓarayi

by DAGA ABBA MUHAMMAD
March 17, 2020
in Labarai
0
Malam Abdullahi Yahaya Maizare

Malam Abdullahi Yahaya Maizare

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
SANANNEN marubucin nan kuma mashiryin finafinai, mazaunin Zariya a Jihar Kaduna, Malam Abdullahi Yahaya Maizare, a yau ya samu kuɓuta daga hannun ɓarayi masu garkuwa da mutane.
 
Hakan ya biyo bayan kuɗin diyya da iyalan sa su ka biya ɓarayin da ke riƙe da shi.
 
Majiyar mujallar Fim ta ce a yau Talata aka tsince shi magashiyan a wani wuri, amma majiyar ta shaida wa mujallar cewa ba ta san inda aka tsince shi ɗin ba domin a lokacin da iyalin sa su ka kira ta ba ta jin su sosai, domin su na ta kuka.
 
Sai dai matar sa ta ce ya dawo ba shi da lafiya, don ko magana ba ya iya yi, har an kwantar da shi a asibiti.
 
Idan kun tuna, a makon jiya mujallar Fim ta ba ku labarin yadda ɓarayin su ka sace Maizare a daren Asabar, 7 ga Maris, 2020 lokacin da ya je karɓo kuɗin hayar gidan wani maigidan sa a Sabon Garin Zariya.
 
Da farko ɓarayin sun buƙaci sai an biya naira miliyan N10 za su sako shi, daga baya su ka rage kuɗin zuwa miliyan 5, sannan kuma sai aka samu matsaya da su cewa rabin miliyan za a biya.
 
A shekaranjiya Lahadi ɓarayin su ka buga wa iyalin waya, su ka ce ranar Talata ce ƙarshe, ko a biya su kuɗin ko su kashe shi.
 
A jiya ɗan sa mai suna Abba ya kai masu kuɗin, waɗanda aka tara ta hanyar karo-karo.
 
Wasu daga cikin marubuta da kuma wasu membobin haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu shirya finafinai ta ƙasa, MOPPAN, su na daga cikin waɗanda su ka bada gudunmawar kuɗin diyyar.
 
Marubutan sun haɗa da Aunty Sadiya Kaduna, Fatima Ɗanbarno, Ibrahim Sheme, da sauran su.
 
Masu shirya finafinai kuma sun haɗa da shugaban MOPPAN na ƙasa, Dakta Ahmad Sarari da sakataren ƙungiyar, Al-Amin Ciroma, da shugabar ƙungiyar a reshen Jihar Kaduna, Hajiya Fatima Lamaj.

Loading

Previous Post

Ladi Mutukaraba ta rasu

Next Post

Lamaj ta kai wa Maizare gudunmawa a asibiti

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Lamaj tare da Ɗanmaliki lokacin ziyarar su ga Maizare a asibiti

Lamaj ta kai wa Maizare gudunmawa a asibiti

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!