• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Masana sun zaburar da matasa kan sanin harshen Ingilishi

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
December 30, 2019
in Marubuta
0
Dama zuwa hagu: Farfesa Munzali Jibril, Farfesa Abdalla Uba Adamu da Dakta Bala Muhammad

Dama zuwa hagu: Farfesa Munzali Jibril, Farfesa Abdalla Uba Adamu da Dakta Bala Muhammad

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MASANA a Kano sun yi kira ga matasan Arewa da su tashi tsaye wajen neman ilimin harshen Turanci domin cin moriyar rayuwar zamani.

 Sun faɗi haka ne a wajen taron gabatar da wani littafi mai suna “The 1000 Words Via Freedom Radio,” wanda marubuci kuma furodusan finafinai Malam Kabiru Musa Jammaje ya wallafa.

 An yi taron a ranar Litinin, 30 ga Disamba, 2019 a Gidan Mambayya da ke unguwar Gwammaja a cikin birnin Kano.  

Taron, wanda shi ne irin sa na farko da shahararren marubucin na Turanci ya shirya, ya yi cikar ƙwari har ta kai babu wajen zama.

 Tun da farko, babban baƙo mai jawabi, Farfesa Munzali Jibril, ya bayyana muhimmancin ilimi a rayuwar matasa, musamman ma a wannan lokaci da duniya ta zamo a waje guda.

 Ya ce wajibi ne matasa su nemi ilimi domin tafiyar da rayuwar su bisa tsarin da zamani ya ke tafiya a kai yanzu. 

Fargesan, wanda malami ne a Jami’ar Bayero, Kano, ya ƙara da cewa, “Koyon yare a yanzu kamar Turanci abu ne da ya zama dole a rayuwa saboda yadda ya mamaye komai na rayuwa. Don haka idan za ka koyi Turanci, to abu mai muhimmancin shi ne sanin yadda za ka furta shi…  

“Don haka a nan ya zama wajibi a yaba wa Kabiru Musa Jammaje saboda ƙoƙarin da ya ke yi ta hanyoyi da dama domin samar wa matasa ingantacciyar hanyar koyon Turanci a cikin yanayi mai sauƙi.” 

Shi ma da ya ke jawabi, tsohon shugaban Hukumar A Daidaita Sahu ta Jihar Kano kuma malami a Jami’ar Bayero, Dakta Bala Muhammad, ya nuna takaicin sa dangane da halin da ilimi ya shiga a yau, ya na mai kira ga gwamnati da cewa abin da ya kamata ta yi a yanzu shi ne “a daidaita sahun ilimi, ba wai a daidaita sahun mashin ba.”

 Shi kuma a nasa tsokacin, shugaban Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN), Farfesa Abdalla Uba Adamu, ya yaba da ƙoƙarin da Jammaje ya yi na samar da wannan littafi, ya na mai cewa samar da littafin ya zo a daidai lokacin da ake buƙatar sa.

 Wasu malaman da fitattun mutanen da dama su ma sun yi muhimman bayanai a wajen, yayin da daga ƙarshe aka bada littafin ga mutanen da su ka halarci taron.

 A jawabin sa bayan an kammala taron, Jammaje ya yi godiya ta musamman ga mahalarta taron tun daga kan malamai da su ka yi jawabai har zuwa sauran mahalarta, da kuma waɗanda su ka bada gudunmawa domin ganin an gudanar da taron. 

Daga ƙarshe, ya yi fatan Allah ya kai kowa gidan sa lafiya. 

Ɗakin taron ya yi cikar ƙwari

Loading

Previous Post

An kasafta sama da N5m don ceto rayuwar Magajiya Ɗambatta

Next Post

Mansurah Isah: Babbar matsalar da na ke fuskanta wajen tallafa wa mabuƙata

Related Posts

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 
Marubuta

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 

January 1, 2025
Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 31, 2024
‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 20, 2024
Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai

November 30, 2024
Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau
Marubuta

Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau

November 27, 2024
Ƙungiyar matasa da mata za ta naɗa Ado Gidan Dabino Sarkin Mawallafan Arewa
Marubuta

Gasar rubutu: Hukumar Tace Finafinai ta bayyana gwaraza 50 na zagayen farko

November 24, 2024
Next Post
Mansurah Isah

Mansurah Isah: Babbar matsalar da na ke fuskanta wajen tallafa wa mabuƙata

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!