• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

MOPPAN da AFMAN kaɗai mu ka yarda su yi wa ‘yan fim sabuwar rajista, inji El-Mustapha

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
August 22, 2023
in Labarai
0
Alhaji Abba El-Mustapha

Alhaji Abba El-Mustapha

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHUGABAN Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, ya bayyana cewa Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN) da Kungiyar Masu Shirya Finafinai ta Arewa (AFMAN) su ne gwamnati ta yarda da su su yi wa kowane ɗan fim ɗin Hausa rajista.

 Ya faɗi haka ne a lokacin da ya ke yi wa mujallar Fim ƙarin bayani kan yadda hukumar sa za ta yi wa ‘yan Kannywood rajista.

Idan kun tuna, jim kaɗan bayan ya ɗare kujerar shugabancin hukumar ya ba da sanarwar cewa hukumar za ta ba da lasisin ga duk wani mai sana’a a cikin kannywood, amma daga baya ya damka alhakin sabunta lasisin a hannun ƙungiyoyin ‘yan fim.

Tun daga lokacin jama’a su ke tambayar lokacin da za a fara yin rajistar da tsarin za a bi wajen sabuntawar.

A hirar sa da wakilin mu a ofishin sa kan al’amarin, El-Mustapha ya ce, “Wannan dama ce ta ƙungiyoyi da tun a baya su ka rasa, wadda a yanzu mu ka mayar musu da ita, saboda ‘yan fim su su ka san kan su a ƙungiyance, don haka zai fi sauƙi idan su su ka tantance kan su.”

Sai dai ya ce duk da haka damar da aka ba ƙungiyoyin, hukumar ba za ta zuba masu ido ba.

“Za mu samar da wakilai masu saka ido don ganin aikin ya tafi daidai, don haka akwai wakilai daga Hukumar Tace Finafinai, Hukumar Hisbah, Hukumar Shari’a da za su yi aiki tare don ganin abin ya tafi daidai,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, “Akwai ƙungiyoyi na ‘yan fim da yawa, amma dai a yanzu mun zaɓi ƙungiyar MOPPAN da ta Arewa domin gudanar da aikin wanda a ƙarƙashin su ne duk wani ɗan fim zai yi rajista ya zama halastaccen ɗan fim da hukuma a Jihar Kano za ta yarda da shi.

Kuma abin da na ke so mutane su sani, mun zaɓi waɗannan ƙungiyoyin guda biyu ne domin samun daidaito, domin da wuya ka samu wani ɗan fim a Kano da ba ya cikin waɗannan ƙungiyoyin.

“Ni kai na ai ka ga akwai ƙungiyar mu ta AHPIP kuma ta na nan har yanzu, akwai ƙungiyoyin mata ‘yan fim; duk ban saka su ba saboda ba na so abin ya yi yawa don kada ya haifar da rashin tsari. Don a yanzu so mu ke mu ga an haɗe kan ‘yan fim don su zama tsintsiya-maɗaurin-ki-ɗaya.

“Kuma ka gane, ni ɗan fim ne da na ke a matsayin jarumi, darakta, furodusa, don haka duk wani abu da ake gudanarwa a cikin harkar na sani. Duk wanda zai zo mana da wasa ba za mu saurara masa ba. Za mu yi abin mu ne cikin tsari domin samun nasarar da mu ke buƙata.”

Loading

Previous Post

Kannywood: Abin da ya sa na tafi na dawo – Alhassan Kwalle

Next Post

Don in cike gurbin adabi ne zan fitar da littafin waƙoƙi na mai suna ‘Dausayin Fasaha’ – Gidan Dabino

Related Posts

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry
Labarai

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry

June 15, 2025
Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
Next Post
Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON

Don in cike gurbin adabi ne zan fitar da littafin waƙoƙi na mai suna 'Dausayin Fasaha' - Gidan Dabino

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!