• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mun kwaso ‘yan Nijeriya 376 daga Sudan, kuma ba za mu bar ko mutum ɗaya a baya ba – Sadiya Farouq

by DAGA WAKILIN MU
May 4, 2023
in Nijeriya
0
Hajiya Sadiya Umar Farouq ta na marhabin ga waɗanda aka dawo da su Abuja daga Sudan

Hajiya Sadiya Umar Farouq ta na marhabin ga waɗanda aka dawo da su Abuja daga Sudan

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

JIMILLAR ‘yan Nijeriya 376 da su ka maƙale a ƙasar Sudan sun iso Abuja lafiya sakamakon aikin kwaso su da Gwamnatin Tarayya ke yi. 

Mai ba da shawara ga Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Miss Nneka Anibeze, ita ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta ba manema labarai a ranar Alhamis.

Ta ƙara da cewa kashin farko na mutanen da aka kwaso, wato mutum 94, sun sauka ne a daren ranar Laraba a jirgin Rundunar Mayaƙan Sama na Nijeriya samfurin Hercules C-130, yayin da sauran mutum 282 su ka sauka a jirgin kamfanin Air Peace. 

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta tsaya a filin jirgin sama na Abuja domin tarbar waɗanda aka ceto daga Sudan ɗin.

A jawabin maraba da ta yi masu, ministar ta yi godiya ga Gwamnatin Tarayya saboda tattaunawar fahimtar juna da ta yi da gwamnatin Sudan wadda har ta kai ga samun karɓar ‘yan Nijeriya tare da kwaso su daga ƙasar da yaƙi ya ɓarke.

Ta ce: “Mun yi murna da ganin sun iso lafiya kuma babu wani rai da ya salwanta. Sun sha matuƙar wahala amma mun gode wa Allah da su ka iso gida lafiya. 

“Mu na gode wa Gwamnatin Tarayya saboda nasarar da aka samu a aikin ceto ‘yan Nijeriyar da ke Sudan. Mu na addu’ar a samu zaman lafiya a Sudan da ma kowane ɓangare na ƙasar nan. 

“Yaƙi ba abu ne mai kyau ba. Kun dai ga yadda mutanen da su ka tafi karatu su ka zama ‘yan gudun hijira ba zato ba tsammani. Wannan ba kawai bala’i ne na ƙasa da ƙasa ba, a’a, bala’i ne kuma da ya shafi jinƙan rayuwar bil’adama. 

“Za mu ba ko wannen su kuɗi N100,000 domin su yi kuɗin mota zuwa wajen iyalan su. Haka kuma mun tanadar da masauki a otal ga waɗanda aka kwaso ɗin har sai sun haɗu da iyalan su, yayin da kuma waɗanda ke buƙatar a duba lafiyar su an yi masu hakan.“

Minista a cikin jirgin Air Peace jim kaɗan bayan saukar ‘yan Nijeriya a Abuja

Minista Sadiya kuma ta bayyana cewa kamar yadda Shugaba Muhammadu Buhari ya umarta, babu wani ɗan Nijeriya da ke son ya tsere daga halin da ake ciki a Sudan da za a bar shi a baya.

Ta ce, “Ma’aikatar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa da kuma Ma’aikatar Harkokin Ƙasashen Waje da sauran ma’aikatun gwamnati irin su NEMA, NCFRMI, NIDCOM, NIA da Rundunar Mayaƙan Sama na Nijeriya su na aiki tare da Ofisoshin Jakadancin Nijeriya da ke Sudan, Masar, Etofiya da Chadi domin tabbatar da cewa ko mutum ɗaya ba a baro ba. Don haka, dukkan ɗan Nijeriyar da ke so ya tsere daga halin da ake ciki a Sudan za a dawo da shi gida cikin tsaro da darajtawa. 

“Aikin kwashe mutanen ya gudana ne ta hanyoyi masu wuyar sha’ani na wasu mutane da su ka zama dillalai a lamarin, wanda hakan ne ya sa aka riƙa fuskantar matsalolin da aikin ya ci karo da su. An shirya ci gaba da kwaso mutanen mu kuma aikin zai gudana da sauri-sauri fiye da da har sai an kwashe dukkan ‘yan Nijeriya da ke Sudan an kawo su gida.”

Ita dai Sudan, ta auka cikin rikicin yaƙi ne a ranar 15 ga Afrilu lokacin da wasu sassa na sojojin ƙasar masu adawa da juna su ka fara kai wa juna hari a birnin Khartoum da yankin Darfur.

Loading

Previous Post

Gamsasshen Bayani Game Da Maguzawan IPOH

Next Post

Ɗangwal da A’isha sun haifi A’isha ‘Yargwal

Related Posts

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Next Post
'Yangwal tare da 'yar su, A'isha 'Yargwal

Ɗangwal da A'isha sun haifi A'isha 'Yargwal

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!