• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mun shirya wa yin zaɓen cike gurbi a Neja, cewar INEC da ‘yan sanda

by DAGA WAKILIN MU
February 5, 2021
in Nijeriya
0
Mun shirya wa yin zaɓen cike gurbi a Neja, cewar INEC da ‘yan sanda
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

Kwamishinan Zaɓe mai zama a Jihar Neja (REC), Farfesa Samuel Egwu, ya ce Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta gama shiryawa tsaf domin gudanar da zaɓen cike gurbi da za a yi a Mazaɓar Tarayya ta Magama/Rijau da ke jihar a ranar Asabar, 6 ga Fabrairu, 2021.


Egwu ya faɗi haka ne a ranar Alhamis lokacin da ya ke tattaunawa da wakilin Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN) a Minna.


Ya ce hukumar sa ta gama duk wani shirin yin zaɓe mai inganci da tsare gaskiya, domin kuwa ta horas da ma’aikatan zaɓe mutum 1,258 saboda zaɓen.

Ya ƙara da cewa masu zaɓe da aka yi wa rajista mutum 159,347 za su kaɗa ƙuri’ar su a rumfunan zaɓe 307, kuma har masu zaɓe guda 158,624 sun karɓi katin su na zaɓe na dindindin.


Egwu, wanda ya ce har hukumar tasa ta gama rarraba kayan da za a yi aiki da su a zaɓen, ya bayyana cewa ya na da tabbacin za a gudanar da zaɓen cikin nasara. 

Ya ce: “Mun gama shirya ma’aikatan mu tare da ba su horo kan sanin makamar aiki ta yadda za su gudanar da zaɓen cikin inganci da tsare gaskiya idan ranar 6 ga Fabrairu ta zo.”

Shi ma Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Neja ya bada tabbacin cewa sun gama duk wani shiri na bada tsaro a lokacin zaɓen ciken gurbin. 


Kwamishinan, Alhaji Adamu Usman, ya faɗi haka ne a lokacin zantawar sa da Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN) a Minna a ranar Alhamis.


Usman ya ce ‘yan sanda tare da sauran hukumomin tsaro da ke jihar su na aiki tare don tabbatar da an yi zaɓen ba tare da wata hatsaniya ba. 

Ya ce: “Mun tura isassun ma’aikata masu ɗauke da makamai domin inganta yanayin siyasa kafin da lokacin da kuma bayan zaɓen.


“Ina bada tabbaci ɗari bisa ɗari ga duk mazauna wannan mazaɓar masu son bin doka da oda cewa za su iya zuwa su kaɗa ƙuri’un su a ranar 6 ga Fabrairu ba tare da fargabar barazana ga rayukan su ko dukiyoyin su ba.”

Previous Post

INEC za ta samar da sabbin rumfunan zaɓe a faɗin Nijeriya kafin zaɓen 2023 – Mahmoud Yakubu

Next Post

Ciwon daji: An damu da shi kuwa?

Related Posts

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Next Post
Ciwon daji: An damu da shi kuwa?

Ciwon daji: An damu da shi kuwa?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!