• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Nafisa Abdullahi ta tayar da ƙura kan yawan haihuwar ‘ya’ya barkatai

by DAGA ABBA MUHAMMAD
April 17, 2022
in Labarai
0
Nafisat Abdullahi

Nafisat Abdullahi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCIYAR jaruma Nafisa Abdullahi ta sake tayar da ƙura a soshiyal midiya, inda ta yi kira ga masu haihuwar ‘ya’ya ba tare da kula da su ba da su guji yin haka.

Jarumar ta bayyana haka ne a wani saƙo da ta wallafa a shafin ta na Tuwita ranar Asabar, 16 ga Afrilu, 2022 inda ta ce, “Ku daina haihuwar ‘ya’yan da ku ka san ba ku da halin kula da su.”

Ta ƙara da cewa, “Allah zai tuhumi mutanen da su ke haifar ‘ya’ya ba tare da sauke nauyin da ya ɗora masu ba.

“Kun ga dukkan mutanen da ke haifar ‘ya’yan da ba su ji ba, ba su gani ba domin kawai su aika da su almajiranci, kuma su ci gaba da haifar ƙarin ‘ya’ya, Allah sai ya saka wa yaran nan!”

Nafisa ta bayyana matuƙar ɓacin ran ta kan yadda wasu iyayen su ke tura ‘ya’yan su ‘yan shekara biyu zuwa uku almajiranci.

Jarumar ta taɓo inda ke yi wa jama’a da dama ƙaiƙayi, domin wannan lamari ne da ya daɗe ya na ɓata wa mutane da dama rai, musamman ganin cewa wasu na zargin ana amfani da irin waɗannan yara wajen aikata laifuka. 
Sai dai kalaman jarumar sun tada ƙura matuƙa, domin sun jawo ce-ce-ku-ce, inda wasu ke yabon ta, wasu kuma na sukar ta.

A shekarun baya akwai wasu daga cikin gwamnonin Arewa da su ka so a dakatar da barace-barace, musamman irin na makarantun allo, sai dai a lokacin waɗanda ke da ruwa da tsaki a harkar makarantun allo su na ganin kamar za a toshe masu hanyar cin abincin su ne, har wasu daga cikin manyan ke faɗin cewa gwamnati ta na shirin faɗa da Allah ne in dai su na hana bara.

Amma kuma in aka koma magana ta gaskiya, akwai matsaloli da dama a cikin lamarin. Domin mutum ne zai haifi sama da ‘ya’ya goma, amma dukkan su bai san yadda su ke rayuwa ba, ya ɗauke su ya kai su wani gari karatun allo, a can ɗin kuma sai sun yi bara kafin su ci abinci. Wasu yaran ba su wuce ‘yan shekara uku zuwa biyar ba.

Don haka idan aka dubi maganar da Nafisa Abdullahi ta yi, lallai ta na da gaskiya. Dole mahukunta su dubi wannan lamari don neman yadda za a magance shi.

Loading

Tags: almajirancihaihuwamakarantar allonafisat abdullahipopulation explosiontazarar iyali
Previous Post

Adam A. Zango ya yi wa aminan sa, Kochila da Sabzor kyautar motoci

Next Post

An raɗa wa ɗan Fati Ladan suna

Related Posts

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry
Labarai

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry

June 15, 2025
Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
Next Post
Yerima Shettima rungume da ɗan sa Amir

An raɗa wa ɗan Fati Ladan suna

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!