• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Nijeriya ta buƙaci haɗin gwiwar ƙasashe don magance matsalar gudun hijira da shige-da-fice

by DAGA WAKILIN MU
October 12, 2022
in Nijeriya
0
Hajiya Sadiya Umar Farouq a taron na UNHCR

Hajiya Sadiya Umar Farouq a taron na UNHCR

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

NIJERIYA ta yi kira ga ƙasashen duniya da su tattaru su haɗa kai wajen neman hanyoyin magance matsalolin da su ka danganci shige-da-fice da gudun hijira.

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji Da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ita ce ta yi wannan kiran a jawabin da ta gabatar a ranar Litinin a wajen Taro na 73 na Babban Kwamitin Gudanarwa na Kwamishinan Hukumar ‘Yan Gudun Hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNHCR) a birnin Geneva. 

Mai tallafa wa ministar a aikin jarida, Miss Nneka Ikem Anibeze, ta ruwaito cewa Hajiya Sadiya ta bayyana irin ƙoƙari da kuma da tsare-tsaren da gwamnatin Nijeriya ta ke fito da su domin inganta ayyukan agaji a Nijeriya musamman ma kan batun ‘yan gudun hijira da masu shige-da-fice tsakanin ƙasashe da kuma ‘yan gudun hijira na cikin ƙasa.

Ministar ta yi kira ga ƙasashe masu ruwa da tsaki a lamarin da su guji nuna bambanci da wariyar launin fata domin gina zaman lafiya mai ɗorewa tare da inganta hanyoyin samun abinci ga al’umma mabuƙata.

Ta ce: “Nijeriya ta na kira ga ƙasashe da su haɗa gwiwa tare da haɗa kai da ɗaukar nauyi da zama tsintsiya maɗaurin ki ɗaya musamman a kan yadda matsalar ke shafar ƙasashe inda ‘yan gudun hijira ke fitowa da ƙasashen da ke karɓar su. Wannan ya yi daidai da sadaukarwar mu a matsayin membobin Yarjejeniyar Ƙasashe Kan ‘Yan Gudun Hijira.

“Nijeriya ta yabi ƙoƙarin UNHCR. Mu na kuma kira ga UNHCR da sauran masu ruwa da tsaki kan batun shige-da-fice da su ci gaba da su haɗa hannu da gwamnatin Nijeriya domin a daidaita tsare-tsare da manufofin mu na cigaban ƙasa da muradan ta.

“Matsalar da ake samu daga sauyin yanayi a Fadamar Tafkin Chadi ta haifar da ƙarin yawan mutanen da aka tilasta wa barin yankin.”

Ta lura da cewa a cikin ‘yan lokutan nan ambaliya da sauran manyan al’amuran sauyin yanayi sun ba da gudunmawa ga ƙaruwar ‘yan gudun hijira.

Ta ce, “A namu ɓangaren na gwamnati, mu na aiwatar da Shirin Ko-ta-kwana na Samar da Abincin Gaggawa domin inganta shiryawa da ƙarfafawa ga al’umma kamar yadda aka tsara a Tsarin Sendai.”  

Hajiya Sadiya ta ce: “Mu na neman a haɗa gwiwa domin a rage tare da shirya zama da sauyin yanayi musamman a wajen batun tilasta wa mutane barin waje.

“Wariyar launin fata da nuna bambanci ba abubuwa ne da za a bar su su samu gindin zama a duniyar mu ta yau ba idan har mu na so mu gina zaman lafiya mai ɗorewa, samar da arziki da kuma inganta sana’o’i da juriya ta yadda za a kyautata ƙasa tare da kare al’umma marasa ƙarfi.”

A ƙarƙashin Yarjejeniya Uku da aka rattaba tsakanin Nijeriya, Kamaru da UNHCR, sama da ‘yan gudun hijira 5,000 ‘yan Nijeriya aka sake dawowa da su cikin ƙasar su bisa amincewar su.

Ta ce a cikin shekaru shidda da su ka gabata, Nijeriya ta samu ƙarin yawaitar masu neman mafaka da ‘yan gudun hijira daga ƙasashe da ke maƙwabtaka da mu. 

Yanzu haka Nijeriya ta na mai masaukin baƙi na ‘yan gudun hijira su 84,314 da masu neman mafaka daga ƙasashe sama da 34, ga kuma ƙarin sama da ‘yan gudun hijira 5,000 daga Kamaru waɗanda ba su da rajista, waɗanda su ka iso kwanan nan. 

“Akwai ‘yan gudun hijira ‘yan Nijeriya kimanin 341,642 a ƙasashen Nijar, Chadi da Kamaru,” inji ta.

Loading

Tags: Genevagudun hijiragwamnatin Nijeriyahadin gwiwaHajiya Sadiya Umar Farouqkasashen duniyamafakaMajalisar Dinkin Duniyashige-da-ficeTaroTsarin SendaiUNHCR
Previous Post

Yadda rubutun littafi ya buɗe mini hanyar kasuwancin soshiyal midiya – JUT

Next Post

Ali Nuhu ya maka jaruma Hannatu Bashir a kotu bisa zargin cin zarafi

Related Posts

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista
Nijeriya

Nijeriya tana kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki da dawo da martabar ƙasa — Minista

June 13, 2025
Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Next Post
Ali Nuhu da Hannatu Bashir

Ali Nuhu ya maka jaruma Hannatu Bashir a kotu bisa zargin cin zarafi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!