• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 20, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Rashin tsaro: INEC ta tsaida aikin rajistar zaɓe ƙananan hukumomi 5 a Filato

by DAGA WAKILIN MU
August 17, 2021
in Nijeriya
0
Rashin tsaro: INEC ta tsaida aikin rajistar zaɓe ƙananan hukumomi 5 a Filato
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta dakatar da aikin rajistar masu zaɓe da ake yi a faɗin ƙasar nan a ƙananan hukumomi biyar na Jihar Filato.

A wata sanarwa da Madam Caroline Okpe, Sakataren Gudanarwa ta INEC, ta fitar a madadin Kwamishinan Zaɓe mai zama a jihar (REC), a ranar Litinin a Jos, ta ce an ɗage aikin ne saboda dokar hana zirga-zirga da gwamnatin jihar ta saka.

Ta ce, “Ɗage aikin zai shafi cibiyoyin rajistar a ƙananan hukumomin Barkin Ladi, Bassa, Jos ta Gabas, Jos ta Arewa da kuma Riyom har sai hali ya yi.

“INEC ta na tabbatar wa da sababbin masu zaɓe da waɗanda ke da matsala da katin su cewa za a yi masu aikin da zarar yanayin ya inganta.”

Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN) ta ruwaito cewa an samu matsalar rashin tsaro ne a wasu sassa na garin Jos, wadda ta kai ga kisan gillar da aka yi wa wasu matafiya waɗanda ba su ji ba ba su gani ba, a Hanyar Rukuba da ke cikin Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa.

An ce matafiyan su na kan hanyar su ne ta dawowa daga taron Zikiri na shekara-shekara da ake yi a Bauchi lokacin da wasu mutane da ‘yan sanda su ka ce “‘yan iskan gari ne” su ka far masu.

Shugaba Muhammadu Buhari da gwamnoni a faɗin ƙasar nan sun yi Allah-wadai da kisan gillar kuma sun yi kira ga jami’an tsaro da su gano waɗanda su ka aikata ta’asar.

Madam Okpe ta ce tilas ne INEC ta tsayar da aikin rajistar domin ba za ta iya ci gaba da shi ba saboda wannan matsala abar baƙin ciki ta rashin tsaro, wadda ta tilasta wa gwamnatin Jihar Filato ta saka dokar hana yawo ta awa 24 a Jos ta Arewa.

Haka kuma gwamnatin jihar ta ƙaƙaba dokar hana yawo daga ƙarfe 6 na yamma zuwa ƙarfe 6 na safe a ƙananan hukumomin Bassa da Jos ta Kudu saboda waɗannan hare-haren.

Madam Okpe ta ce INEC za ta tabbatar da cewa dukkan ‘yan ƙasa da su ka cancanta a jihar za a yi masu rajista idan halin da ake ciki ya gyaru.

Loading

Tags: Caroline OkpeContinuous Voter RegistrationHukumar Zabe ta KasaIndependent National Electoral CommissionINECJos killingsProfessor Mahmood Yakubu
Previous Post

Auren mawaƙin Kannywood Garzali Miko da Habiba ya zo

Next Post

INEC ta samu buƙatun rajistar zaɓe miliyan 2.4, yayin da an yi rajistar mutum miliyan 1.9 ta yanar gizo

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
INEC ta samu buƙatun rajistar zaɓe miliyan 2.4, yayin da an yi rajistar mutum miliyan 1.9 ta yanar gizo

INEC ta samu buƙatun rajistar zaɓe miliyan 2.4, yayin da an yi rajistar mutum miliyan 1.9 ta yanar gizo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!