• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Rasuwar Umar Sa’idu Tudunwada ta shafi rayuwa ta, cewar Baharu

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
July 10, 2019
in Tattaunawa
0
Balarabe Murtala Baharu (a dama) tare da Umar Sa'idu Tudunwada a lokacin naɗin Umar a matsayin Ɗanmasanin Tudunwada kwanan baya

Balarabe Murtala Baharu (a dama) tare da Umar Sa'idu Tudunwada a lokacin naɗin Umar a matsayin Ɗanmasanin Tudunwada kwanan baya

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ALHAJI Umar Sa’idu Tudunwada ƙwararren ɗan jarida ne wanda ya taɓa aiki a Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA) a Washington DC, kuma ya taɓa zama shugaban gidan Rediyo Freedom da ke Kano. A lokacin rasuwar sa, shi ne shugaban gidan Rediyo Kano. Ya rasu a ranar Lahadi, 30 ga Yuni, 2019 a wani haɗarin mota da ya ritsa da shi tare da matar sa Hajiya A’ishatu Sule da ‘yar sa Maryam da direban sa Malam Ado Gauta a cikin garin Kura, Jihar Kano, a kan hanyar su ta dawowa daga Abuja, amma shi kaɗai ya rasu. 

Kafin rasuwar sa, ya ɗauki nauyin shirya fim mai nisan zango (‘series’) mai suna ‘Bilkisu’ a ƙarƙashin kamfanin sa na Amara.

Daraktan fim ɗin ‘Bilkisu’, Malam Balarabe Murtala Baharu, ya yi hira da mujallar Fim inda ya bayyana irin alhinin da ya shiga sakamakon rasuwar ubangidan nasa, kuma ya bayyana irin gudunmawar da marigayin ya ba Kannywood. Ga hirar: 

FIM: Ka na ɗaya daga cikin manajojin kamfanin shirya finafinai na Amara, sannan kai ne daraktan fim ɗin ‘Bilkisu’, duka na marigayi Umar Sa’idu Tudunwada. Ko yaya ka samu kan ka a sakamakon jin labarin rasuwar sa?  

BAHARU: To gaskiya ina ganin zan iya cewa ina ɗaya daga cikin waɗanda za a ce an yi masu rasuwar sa, saboda ya riƙe ni tamkar ɗan sa kuma ya ba ni damar da ba kowa ya same ta ba, ko da a cikin ’ya’yan sa ne. Don ya horar da ni mu’amala da mutane kuma ya nuna min tsayawa a kan gaskiya da kyautata wa mutane, kuma ya ɗauki amanar aikin da ya ke ganin al’umma za su kalla wanda zai zama ma’auni ta hanyar fim da zai canja harkar finafinan Hausa ya ba ni. Don haka wannan ta sa  na ke ganin ba ni aikin ‘Bilkisu’ da ya yi na zama a matsayin mai shiryawa nashi  da bada umarni wannan shi ne abin da ba zan taɓa mantawa da shi a rayuwa ta ba.  

FIM: Da yake fim ɗin ‘Bilkisu’ bai riga ya fito ba, ko ina matsayin fim ɗin a yanzu?

 BAHARU: To farko dai matsayin fim ɗin a yanzu ana matakin yanka hotunan da tace su, don haka an zo gaɓar ƙarshe ta kammaluwar aikin gaba ɗaya. Sai dai abin juyayi da alhini a kan wannan aikin shi ne marigayi bai taɓa zama ya kalli aikin ya ga ina aka tsaya ba. Sai dai ya kalli wani ɓangare na abin da aka ɗauko a lokeshin. Sai kuma sinasinai biyu da aka tace na ɗauka a waya na je na nuna masa, sai kiɗan bayan fage da na ɗauka ya yi masa zai saka a kwamfutar sa ya rinƙa ji. Abin da na sani kenan.  

Kuma a yanzu bisa hasashe da mu ke yi, ba ma aikin ‘Bilkisu’ ba, duk wasu aikace-aikace na kamfanin Amara ba ma fatan abin zai tsaya da yardar Allah. Amma dai abu ne na magada, sai hukuncin da su ka yanke. Kuma a yanzu haka akwai mutanen da ya raina da su ke ƙoƙarin ganin wannan aiki na ‘Bilkisu’ ya kammala.

 Kuma ƙarin bayanin da zan yi maka shi ne abubuwan da Umar Sa’id Tudunwada ya yi a harkar fim sai nan gaba za su ƙara fitowa, domin shi ne mutum na farko da ya ke kare masana’antar daga dukkan wani abu da zai taso mata na damuwa ba tare da ’yan fim sun sani ba. Kuma ya tsaya wajen ganin an tabbatar da zaɓen MOPPAN wanda ya gabata a Kano, kuma shi ne ya bada ofishin sa domin a rinƙa horas da ƙananan marubuta labarin fim domin su koya, kuma burin sa ya cika, domin wasu da yawa daga cikin su a yanzu su na cin gajiyar abin. 

Amma abu ɗaya da zan ce ya tafi da burin tabbatuwar sa shi ne wannan fim ɗin na ‘Bilkisu’.

 Ina fatan Allah Ya cika masa burin sa, kuma Allah ya jiƙan sa, ya yafe masa kurakuran sa, ya inganta zuriyar sa. Allah Ya jiƙan Umar Sa’id Tudunwada, amin.

Umar Sa’idu Tudunwada tare da ma’aikata a lokacin rubuta labarin fim ɗin ‘Bilkisu’. Baharu ne daga hagu

Loading

Previous Post

Adamu Ability ya zama mai igiya 3

Next Post

Abubakar ASAS ya tare a sabon gida

Related Posts

Ba faɗuwar zaɓen MOPPAN ta sa muka kafa ƙungiyar NEKAGA ba, inji Ability 
Tattaunawa

Ba faɗuwar zaɓen MOPPAN ta sa muka kafa ƙungiyar NEKAGA ba, inji Ability 

March 1, 2025
Za mu kawo sauyi ga matan Kannywood da tallafin NITDA, inji Mansurah Isah
Tattaunawa

Za mu kawo sauyi ga matan Kannywood da tallafin NITDA, inji Mansurah Isah

November 13, 2024
Bikin auren ‘ya’ya na ya ɗaga daraja ta – Aminu Ala
Tattaunawa

Bikin auren ‘ya’ya na ya ɗaga daraja ta – Aminu Ala

August 2, 2024
Buri na in samar wa MOPPAN tsarin shugabancin da za a riƙa tunawa da ni – Habibu Barde
Tattaunawa

Buri na in samar wa MOPPAN tsarin shugabancin da za a riƙa tunawa da ni – Habibu Barde

March 13, 2024
Mahaifiyar Afakallahu ta kwanta dama
Tattaunawa

Afakallahu: Abin da mahaifiyar mu ta karantar da mu

March 11, 2024
Gaskiyar abin da ya faru gare ni a haɗarin da na yi – Jarumar Kannywood Maryam CTV
Tattaunawa

Gaskiyar abin da ya faru gare ni a haɗarin da na yi – Jarumar Kannywood Maryam CTV

February 14, 2024
Next Post
Fuskar gidan daga ciki

Abubakar ASAS ya tare a sabon gida

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!