• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Rikicin mawaƙa: Ummi B.Y. ta maka El-Mu’az Birniwa a kotu a Kaduna

by DAGA ABBA MUHAMMAD
October 4, 2022
in Labarai
3
Ummi B.Y. da El-Mu'az Birniwa

Ummi B.Y. da El-Mu'az Birniwa

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MAWAƘIYA kuma jaruma a Kannywood, Amina Abdullahi, wadda aka fi sani da Ummi B.Y., ta maka fitaccen mawaƙin nan El-Mu’az Muhammad Birniwa a kotu kan zargin tsoratarwa.

Ta shigar da ƙarar ne a Babbar Kotun Majistare da ke unguwar Rigachikun, Kaduna, a ranar 29 ga Satumba, 2022, ta hanyar lauyan ta, Abdulsaleem Umar na cambar ‘M.T. Mohammed and Co. (Pinnacle Chambers)’ da ke Titin Alƙali, cikin garin Kaduna.

Sammacin ƙarar, wanda mujallar Fim ta samu kwafen sa, ya nuna cewa Ummi ta yi ƙarar El-Mu’az ne bisa babban laifin barazana (direct criminal complaint for the offence of intimidation) wanda ya saɓa wa sashe na 377 na kundin finalkod na Jihar Kaduna na shekarar 2017.

A sammacin, jarumar ta faɗa wa kotun cewa ita mazauniyar garin Birnin Yero ce, yayin da shi El-Mu’az mazaunin Unguwar Kaji ne da ke garin Kaduna, don haka kotun na da hurumin sauraren ƙarar.

Ta ce a ranar 2 ga Satumba, 2022 ta kira wanda ta ke ƙarar a waya domin su gaisa a matsayin sa na abokin hulɗar ta, amma sai kawai ya shiga surfa mata zagi tare da yi mata barazanar sai ya sa yaran sa sun kashe ta kuma babu abin da za a yi tunda ya na da iko a cikin al’umma.

Sammacin ƙarar da Ummi ta kai El-Mu’az

Ta ƙara da cewa a cigaba da barazanar da ya yi mata, da misalin ƙarfe 9 na dare a ranar 22 ga Satumba sai ga wasu ‘yan daba ya turo mata har gida domin su ɗauke ta su tafi da ita zuwa wani waje da ba ta sani ba, amma wasu bayin Allah su ka taimaka mata su ka hana ‘yan iskar shiga gidan.

“Yanzu wadda ke ƙarar ta na fargabar fita daga gida saboda tsoron kada wanda ake ƙarar ko yaran sa su da ya ɗauka su kai mata hari ba tare da wani dalili ba,” inji lauyan ta.

Ya ce a yanzu haka El-Mu’az ya na nan ya na neman Ummin ruwa a jallo a kan tunanin cewar shi wani isasshe ne wanda ko me ya aikata ba za a iya yi masa komai ba.

Lauyan ya nuna wa kotun cewa wannan abu da ake zargin El-Mu’az da aikatawa babban laifi ne wanda ya saɓa wa sashe na 377 na kundin finalkod na Jihar Kaduna na shekarar 2017.

Idan kun tuna, mujallar Fim a makon jiya ta ba da labarin yadda rigima ta kaure a tsakanin mawaƙan biyu.

Loading

Tags: Abdulsaleem UmarAmina MohammedbarazanaBirnin YerofinalkodintimidationKannywoodkotun majistarelauyaM.T. Mohammed and Co.mawaƙaPinnacle ChambersRigachikunUmmi B.Y.Unguwar Kaji
Previous Post

Za mu samar da cibiyar koyar da sana’ar fim a Kano – Gwamna Ganduje

Next Post

Bikin auren jarumar Kannywood Ruƙayya Dawayya da shugaban Hukumar Tace Finafinai, Afakallah ya matso

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Dawayya da Afakallah

Bikin auren jarumar Kannywood Ruƙayya Dawayya da shugaban Hukumar Tace Finafinai, Afakallah ya matso

Comments 3

  1. Pingback: Mawakiya Ummi B.Y ta maka mawaki El-Mu'az Birniwa a kotu kan yi mata barazanar zai sa a kashe ta - Kyauta Blog
  2. Pingback: Mawakiya Ummi B.Y ta maka mawaki El-Mu’az Birniwa a kotu kan yi mata barazanar zai sa a kashe tah - Dailygistnaija
  3. Pingback: Mawakiya Ummi B.Y ta maka mawaki El-Mu’az Birniwa a kotu kan yi mata barazanar zai sa a kashe ta - Mr ATG News.com

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!