• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Sha’iri Aminu Ala ya fito takarar ɗan Majalisar Tarayya a Kano

by DAGA ABBA MUHAMMAD
August 30, 2022
in Labarai
0
Fostar takarar Aminu Ala

Fostar takarar Aminu Ala

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN mawaƙi Aminuddeen Ladan Abubakar (ALA) ya bayyana cewa ya tsaya takarar zama ɗan Majalisar Wakilai ta Tarayya a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar ADP a zaɓen shekarar 2023.

Ya ce ya na neman kujerar memba ne mai wakiltar Mazaɓar Tarayya ta Nassarawa, Kano.

Sha’irin ya bayyana haka ne a saƙwanni uku da ya wallafa a Facebook da Instagram inda ya yi jawabi kamar haka: “Mulki na Allah ne, ya na bai wa wanda ya so a san da ya so. 

“Mun fito da ƙarfin Allah tare da goyon bayan mutane don mu wakilci mutane daga cikin mutane zuwa ga mutane don mutane. Mu na nemar yardar Allah tare da roƙon Allah ya sa mutane su yarda da manufofin matuƙar ba su kauci tafarkin nagarta ba.”

A saƙo na biyu da mawaƙin ya wallafa a soshiyal midiya, ya ci gaba da yin addu’ar cewa: “Kamar yadda Allah ya ba mu damar bayyana kai a rukunin masu shirin wakilcin jama’a, mu na neman tallafawar Allah a cikin dukkan motsi da gilmawar mu a kan wannan ƙudiri.

“Allah ka ƙaddara wannan yunƙuri ya zama alkhairi ga al’umma. 

Wata fostar ɗauke da hotunan Ala da Sha’aban Sharaɗa

“Allah ka sa ya zama cigaban ƙasa ta, Allah ka sa ya zama alfanu a gare ni da al’ummar yankin Nassarawa kafatanin su.

“Cikakken misali ga masu niyyar takara duba da cancanta da nagarta. Masoya ga ranar ku daga duk inda ku ke za ku bai wa wannan tafiya gudunmawa. A duk inda ka ke ba ka rasa ɗan’uwa ko masoyi a Ƙaramar Hukumar Nassarawa ba. 

“Ku zaɓi jam’iyyar ADP, Action Democratic Party, don karya manufar tsarin mulkin bayan-na-yi ɗa-na-ya gaje-ni.”

Haka kuma a rubutun sa na uku Ala ya ce: “Kada ka yi taraddadi da abin da idon ka ya nuna maka zahiri ne.

“Lokaci na a cirata a fidda ɗan takara daga cikin mutane ya yi wakilci don mutane.

“Ka sa a ran ka mulki na Allah ne kuma ya na bai wa wanda ya so.

“Ka sami nutsuwa da ƙarfin gwiwa a kan nasara ta jajirtattun bayi ce waɗanda su ka kamaci kamata.

“Mu na neman goyon bayan ku masoya, kamar yadda ɗimbin nasarori da su ka faru su ke kan faruwa da gudunmawar ku da hannun ku, wannan karon ma mu na neman goyon baya da addu’a a duk inda ku ka kasance.”

Taken takarar Ala dai shi ne: “Mu Gudu Tare Mu Tsira Tare”, wanda ya rubuta a jikin fastocin da ya wallafa tare da saƙwannin.

Wannan takara da ya fito, ya bi sahun abokin sa Dauda Adamu Abdullahi Rarara a ƙarƙashin ƙungiyar 13×13, ganin ADP ce Rarara ɗin ya ke yi a Jihar Kano, inda ya bi ɗan takarar gwamna na jam’iyyar, wato Sha’aban Ibrahim Sharaɗa.

Ɗimbin masoya sun taya Ala fatan alheri da addu’ar samun nasara a wannan niyya da ya ɗaura.

Loading

Tags: ADPAminu AlaDauda RararaKanoMajalisar Wakilai ta TarayyaMazaɓar NassarawaSha'aban Sharaɗasoshiyal midiyatakaraZaɓen 2023
Previous Post

Ayyiririi! Mawaƙiya Hajjo Idi Moris ta yi miji

Next Post

Rarara ya sake sanya gasar waƙar siyasa

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Abubakar Bashir Maishadda

Rarara ya sake sanya gasar waƙar siyasa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!