• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ta’aziyyar Muhammadu Ɗan Sanyinna (Raba-Gardama)

by DAGA FATUHU MUSTAPHA
January 11, 2022
in Al'adu
0
Marigayi Alh. Mamman Raba-Gardama. Hoto daga: Abdulaziz Abdulaziz

Marigayi Alh. Mamman Raba-Gardama. Hoto daga: Abdulaziz Abdulaziz

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

“Ya kai tsaye ga wani ya tsaya
Yanzu gwanin wani zai tafi lahira
Ya kashe ka ya taka ma wuya,
Mu ko mu bi shi a baya da tambura”

– Sarki Usaini a taken Raba-Gardama 

A LOKACIN da mu ke jimamin mutuwar Alhaji Bashir Tofa, Dakta Datti Ahmad, da Sheikh Ahmad Bamba, sai kuma ga shi a daren nan Allah ya karɓi ran ɗaya daga cikin manyan ‘yan damben da tarihin dambe a Nijeriya ba zai taɓa mantawa da su ba, wato Muhammadu Ɗansanyinna wanda aka fi sani da Muhammadu Raba-Gardama. 

Muhammadu ya yi tashe a shekarun 1980 zuwa na 1990, tun bayan da manyan ‘yan dambe irin su Shago, Ɗandunawa da Ado Ɗankore su ka kwanta dama a fagen. Shaharar sa da nasarorin da ya samu a zamanin da ya ke tashe sun sanya ya zama wani abin kwatance a wannan lokaci. 

Ban dai iya tuna ko a wane ɓangare  Muhammadu ya ke a zamanin sa, Kudu ko Arewa, ko Guramaɗa (Jamus) ne. Amma dai ba na zaton Guramaɗa ne, tunda su zallar Fulani ne a cikin su. 

Muhammadu ya zama jagoran wasu manyan ‘yan dambe na zamanin sa, irin su babban hafsan sa, Amadu Gurɗe, Sani Ƙanin Basafce, wanda kowane ɗaya a cikin su babbar gayya ne. 

Koda yake Muhammadu ya yi agar a zamanin sa, amma bai ci karen sa babu babbaka ba, domin sai da ya samu kishiya, wato Duna na Indabo, wanda aka fi sani da Ɗancana, da kuma wasu manyan yaran sa irin su Ciroma Adamu Ɗansarki. 

Muhammadu ya shahara da juriya da rashin tsoro. A iya sani na, in ban da Ɗancana mutum biyu na taɓa sanin sun kashe Raba Gardama a dambe, ɗaya a Sakkwato, ɗaya a Kazaure. 

Na sha ganin damben su da Ɗancana; dambe ne kamar ana yaƙi, kuma kowanne a wannan lokaci shegen kan sa ne. 

Akwai abubuwa biyu da ba na mantawa da su a game da Muhammadu. Na farko rikicin sa da Ɗandunawa a Ɓaɓura, a wannan lokaci ina zaton Ɗandunawa ya haura shekara goma da barin dambe, amma a tsaurin ido na Muhammadu ya nemi sai ya yi dambe da shi. Wannan fitsara da Muhammadu ya yi masa ta sanya Ɗandunawa ya haɗa shi dambe da wani yaron sa daga cikin Guramaɗa, inda su ka yi damben ya buge Muhammadu a Kazaure. Wannan kisa ya rikita Muhammadu ƙwarai, inda ya tare ƙofar shiga sitadiya ɗin, ya hana kowa shiga ko fita, har sai da Sarki Usaini ya zo ya na kaɗa masa taken sa:

“Zuciya tasa in ta birkita, 
Ka ga farar hula ba ta masa, 
Ni makaɗin ma har tsoro na ke!” 

A wannan rikici sai da Muhammadu ya sumar da jami’an ‘yan sanda har biyu a sakamakon ƙoƙarin su na su kama shi. 

Abu na biyu shi ne wani dambe da su ka yi a Sakkwato, inda nan ma bai sa’a ba, aka buge shi. Hakan ta harzuƙa shi, ya nemi lallai a sake damben, amma aka ƙi. Ya hargitsa filin, sai a mota aka sanya abokin damben nasa aka fita da shi. Ganin haka ya bi motar da gudu, ya kai mata naushi, ya samu gilashin motar, duk ya yanke hannu. 

Mamman Raba-Gardama (Ɗansanyinna) ya na matashi. Ya rasu a yau bayan ya yi fama da rashin lafiya, aka yi jana’izar sa da misalin ƙarfe 10:00 na safe a gidan sa da ke shiyyar Gidan Dare bayan gidan ‘Yarnanu Mai Saida Abinci cikin garin Sakkwato. Allah ya jiƙan sa, amin.

Muhammadu mutum ne karimi, mai kyauta, kuma ga iya kwalliya. In ya gama dambe ya ci kwalliya, kai ba ka ce shi ba ne. 

A da, na ɗauka Muhammadu ya rasu, sai a ‘yan shekarun nan aka ce min ya na nan da ran sa, har ma ya kan je kallo. Na so in gamu da shi, domin rabo na da ganin sa tun cikin shekarun 1990 lokacin bai ajiye akayau nai ba. Sai dai Allah bai yi hakan za ta tabbata ba. 

Allah ya jiƙan shugaban damben Nijeria, ya yafe kurakuran sa, ya sa mutuwa hutu ce.

Loading

Tags: Ado ƊankoreAmadu GurɗeCiroma Adamu ƊansarkidambeƊancanaƊandunawaGuramaɗaJamusMamman ƊansanyinnaMuhammadu Raba-GardamamutuwaSakkwatoSani Ƙanen BasafceSarki UsainiShago
Previous Post

An tara naira miliyan 14 a taron ƙaddamar da littattafan Fatima Ibrahim Abba Gana

Next Post

Minista Sadiya ta jajanta wa ‘yan kasuwar Guru da gobara ta yi wa ɓarna

Related Posts

Al'adu

Kare Sabbin Kalmomin Hausa “Saskiyā” (Synonym) da “Gīɗiyā” (Antonym) ta Hanyar ‘Yancin Binciken Ilimi

May 22, 2025
Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II kadara ne mai daraja ga Jihar Kano
Al'adu

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II kadara ne mai daraja ga Jihar Kano

January 28, 2024
Minista Hannatu Musawa ta ƙudiri aniyar kafa Gidan Tarihi da Gidan Wasanni na Ƙasa a Abuja
Al'adu

Minista Hannatu Musawa ta ƙudiri aniyar kafa Gidan Tarihi da Gidan Wasanni na Ƙasa a Abuja

December 14, 2023
Khalifa Muhammadu Sanusi II
Al'adu

Sanusi: Magajin Sanusi da Kukuna

June 23, 2023
Shugabannin ƙasashen Afrika a wajen wani babban taron su a Habasha
Al'adu

Ƙungiyar Tarayyar Afrika ta zaɓi Swahili a matsayin harshen da za ta riƙa aiki da shi

February 10, 2022
Waɗansu 'yanmatan Fulani a ƙasar Benin. Hoto daga: Alamy
Al'adu

Tarihin Fulani: Mahangai huɗu

December 13, 2021
Next Post
Hajiya Sadiya Umar Farouq

Minista Sadiya ta jajanta wa 'yan kasuwar Guru da gobara ta yi wa ɓarna

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!