• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Tarihin Bature Gagare (1958-2002), marubucin littafin ‘Ƙarshen Alewa Ƙasa’

by DAGA KABIR UMAR SAULAWA
July 28, 2019
in Marubuta
0
Malam Bature Gagare da littafin sa na 'Ƙarshen Alewa Ƙasa'

Malam Bature Gagare da littafin sa na 'Ƙarshen Alewa Ƙasa'

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
CIKAKKEN sunan Bature Gagare dai shi ne Ibrahim Lawal. An haife shi a cikin Lamama da ke unguwar Galadunchi a tsakiyar birnin Katsina. Ya yi karatu a Makarantar Firamare ta Gobarau, Katsina (1966-1972), da kuma Kwalejin Barewa, Zariya (1973- 1977). Ya na ɗaya daga cikin haziƙai kuma masu matuƙar ƙoƙari da fahimta, ganewa da cin jarabawa a dukkan karatun da ya yi.
 
Mahaifin Bature, Alhaji Lawal Gagare, asalin sa mutumin Malumfashi ne. Aiki a hukumar Ene (Native Authority) ya kawo shi Katsina. Ya rasu a lokacin Bature na da kimanin shekara biyu da haihuwa.
 
Alhaji Tanimu Gagare Kafinta, mahaifi ga Kabir Tanimu Gagare, shi ne ya riƙe Bature Gagare har ya girma.
 
Binta (Atutu) ita ce mahaifiyar Bature Gagare. Mutunniyar sabon garin Eka ce da ke Ƙaramar Hukumar Rimi ta Jihar Katsina. Mai kimanin shekaru 85, yanzu haka ta na nan raye a garin Kaduna.
 
Sauran ‘yan’uwan Bature Gagare ciki ɗaya sun haɗa da mariganya Binta, mariganyi Aminu, sai mariganya Murja wadda ta rasu a ranar Juma’a, 26 ga Yuli, 2019, kwana biyu kacal bayan na yi hira da ita tare da wani ɗan’uwan ta mai suna Alhaji Ummaru inda na samu bayanai game da marigayi Bature.
 
Bature Gagare, wanda ake yi wa laƙabi da BT, bai yi wani dogon karatun boko ba duk da ƙwaƙwalwa da ƙoƙarin da Allah ya ba shi. Amma ya fara Advanced Teachers College, Kafanchan, a Jihar Kaduna, inda ya jagoranci wata zanga-zanga wadda ta yi sanadiyyar barin karatun nasa. Sai ya dawo gida Katsina, ya fara karatu a Makarantar Aikin Jinya (School of Nursing), to amma a nan ma aka samu wata matsala makamanciyar ta ATC Kafanchan, ya bar karatun.
 
Duk da haka, ya shiga ran malaman sa ƙwarai a dukkan makarantun da ya yi, ganin irin ƙwazon sa da hazaƙar sa a karatu.
 
BT ya yi fice ƙwarai a harkar rubuce-rubuce da tafiye-tafiye. Littafin sabon na hikaya, ‘Ƙarshen Alewa Kasa’, ya yi fice sosai inda a 1980 ya zamo na uku a gasar rubuta ƙagaggun labarai na Hausa ta ƙasa da aka yi a ƙasar nan, inji Dr Garba Ashiwaju a muƙaddimar littafin da ya rubuta lokacin shi ne Daraktan Ma’aikatar Al’adun Gargajiya ta Tarayya.
 
Bature ya rubuta wani littafin da ya sa wa suna ‘Tsuliyar Kowa Da Kashi’, to amma ba a samu damar wallafa shi ba sakamakon taƙaddama da aka yi da shi tun daga sunan littafin har ya zuwa bayanan da ke cikin shi.
 
Wani abu kuma game da Bature Gagare shi ne, shi mutum ne wanda ya iya zane matuƙa; an ce duk abin da ya kalla zai iya zana shi ba tare da kuskure ba balle ɓata lokaci.
 
Ya rayu da mata uku a lokuta daban-daban. Su ne Balaraba, Amina da Saadatu. 
 
Ya na da ‘ya’ya shida, wato Kabir, Asma’u, Amina (Junior), A’isha, Laila da Zainab.
 
Bature mutum ne mai matuƙar tsafta. Kuma ya na son abinci na gargajiya kamar ɗanwake, koko, ƙosai, kwaɗo, alkubus, hura, wake da shinkafa.
 
Kaɗan daga cikin halayen BT sun haɗa da:
 
1. Son gaskiya da kamanta ta.
 
2. Mutum ne marar tsoro.
 
3. Abin shi ko abin duniya ba ya rufe masa ido.
 
4. Ya na da sada zumunci da son mutane.
 
Bayan haka, ya na da abubuwan ta’ajibi da ban-mamaki ƙwarai da gaske.
Ya yi tafiye-tafiye a ciki da wajen Nijeriya a ƙasashe da su ka haɗa da Saudi Arebiya, Aljeriya, Dubai da Maleshiya.
 
Allah ya yi wa Bature Gagare rasuwa a ranar 29/2/2002 a Lamama, Galadunchi, cikin birnin Katsina, sanadiyyar ciwon lamoniya (pneumonia), wato ciwon sanyin huhu. An yi masa sutura a tsohuwar maƙabartar Ɗantakun.
 
Malam Kabir Umar Saulawa (PRO) ya rubuto ne daga Katsina. Lambar waya: 07034610481

Loading

Previous Post

Abubakar ASAS ya tare a sabon gida

Next Post

Zulaihat ZPreety: ‘Ba rawa da waƙa ne ke da muhimmanci a cikin fim ba’

Related Posts

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 
Marubuta

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 

January 1, 2025
Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 31, 2024
‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 20, 2024
Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai

November 30, 2024
Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau
Marubuta

Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau

November 27, 2024
Ƙungiyar matasa da mata za ta naɗa Ado Gidan Dabino Sarkin Mawallafan Arewa
Marubuta

Gasar rubutu: Hukumar Tace Finafinai ta bayyana gwaraza 50 na zagayen farko

November 24, 2024
Next Post
Zulaihat Ibrahim (ZPreety)

Zulaihat ZPreety: 'Ba rawa da waƙa ne ke da muhimmanci a cikin fim ba'

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!