• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, May 18, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Tsohon ɗan jarida Sanda Adamu Tsafe ya kwanta dama

Shekarun sa 77

by ALI KANO
February 9, 2025
in Labarai
0
Tsohon ɗan jarida Sanda Adamu Tsafe ya kwanta dama

Marigayi Alhaji Sanda Adamu Tsafe (Sarkin Yaƙin Tsafe)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ALLAH ya yi wa tsohon ɗan jaridar nan kuma dattijon arziki, Alhaji Sanda Adamu Tsafe, rasuwa. Shekarun sa 77.

Ya rasu a daren jiya a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo (UDUTH) da ke Sakkwato bayan ya yi fama da rashin lafiya.

Marigayi Alhaji Sanda ya yi fice a aikin rediyo a lokacin da yake aiki a gidan Rediyo Talbijin Kaduna.

Daga nan ya yi aiki a Sashen Hausa na gidan rediyon BBC.

Haka kuma ya taɓa zama Janar Manaja na gidan Rediyon Rima da ke Sakkwato, muƙamin da aka tsige shi daga kai sakamakon rikicin sarauta da ya biyo bayan rasuwar Sarkin Musulmi Abubakar na 3 a cikin 1988.

Daga bisani, an naɗa shi Kwamishinan Zaɓe na Tarayya mai kula da Gundumar Birnin Tarayya (FCT).

Alhaji Sanda sananne ne wajen taimakon jama’a da kuma ayyukan addini, musamman a Jihar Zamfara.

‘Yandoton Tsafe Alhaji Habibu Aliyu ya naɗa shi Sarkin Yaƙin Tsafe.

Shi ne ciyaman na kamfanin Adahan Universal Investment Limited.

An haife shi a cikin 1948 a garin Tsafe, inda a nan ya fara yin karatun firamare kafin ya wuce Babbar Makarantar Firamare da ke Kwatarkwashi.

Ya yi karatu a Makarantar Lardi da ke Sakkwato, da Makarantar Share Fage (SBS) ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.

Daga bisani, ya yi karatu a Makarantar Aikin Jarida ta London, wato London School of Journalism.

Marigayi Alhaji Sanda ya rasu ya bar matan aure biyu, da ‘ya’ya 29, da kuma jikoki 36.

Allah ya rahamshe shi, amin.

Marigayi Alhaji Sanda Adamu Tsafe

Loading

Tags: rasuwaSanda Adamu TsafeZamfara
Previous Post

Gwamnatin Tarayya ta ba kamfanin Lenscope Media kwangilar naira miliyan 250 domin gina Gidan Shirya Finafinai na Jos da badalar Kano

Next Post

‘Arewa Republic’. Kun gani ba?

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
‘Arewa Republic’. Kun gani ba?

'Arewa Republic'. Kun gani ba?

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!