• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Tsohon shugaban MOPPAN, Abdullahi Maikano, ya aurar da ‘yar sa ta uku, Rabi’atu

by DAGA ABBA MUHAMMAD
September 15, 2023
in Labarai
0
Alhaji Maikano da 'yar sa, amarya Rabi'atu, a ranar auren ta

Alhaji Maikano da 'yar sa, amarya Rabi'atu, a ranar auren ta

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

TSOHON Shugaban Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), Alhaji Abdullahi Maikano Usman, ya aurar da ‘yar sa ta uku a yau Juma’a.

An ɗaura auren Rabi’atu Abdullahi Maikano da abin ƙaunar ta, Khamis Garba Zarewa, da misalin ƙarfe 2:15 na rana, wato bayan an sauko daga sallar Juma’a, a masallacin Juma’a na Al-Mannar da ke Unguwar Rimi, Kaduna a bisa sadaki N150,000.

Mahaifin amarya ya nuna matuƙar farin ciki, ganin yadda jama’a su ka taru domin ɗaurin auren. Wannan ya sa tun ana shirin ɗaurin auren ya riƙa bi layi-layi a cikin masallacin ya na gaisawa da mutane, ya na kuma yi masu godiya.

Bayan an ɗaura auren, sai aka ɗunguma zuwa sabon gidan Maikano da ke unguwar Babbar Saura, inda aka gudanar da walima.

Sheikh Tukur Adam, babban limamin Masallacin Al-Mannar, shi ne babban baƙo a wurin walimar.

Da farko, Maikano ya buɗe taro da addu’a tare da gabatar da Sheikh Tukur da babban limamin masallacin Jum’a da ke unguwar Babbar Saura, Sheikh Musa Haruna.

Maikano (a dama) tare da aminin sa, furodusa kuma darakta Alhaji Magaji Sulaiman

Sheikh Tukur ya yi taƙaitaccen jawabi a kan muhimmancin aure da kuma jan hankalin ma’aurata da kira ga matasa da su guji auren sha’awa.

Shehin malamin ya yi addu’o’i ga ma’auratan da iyayen su da kuma sauran masu aure da ma waɗanda ba su kai ga yin auren ba.

Haka shi ma Sheikh Musa Haruna, ya yi jawabi ne a kan aure da muhimmancin haƙuri a lokacin da aka shiga matsatsin rayuwa.

Sannan ya yi bayani a kan yadda wasu matan ke jan hankalin mazajen su wurin neman halak, su guje wa haram yayin da su ke nema wa iyalin su abin da za su kula da su.

Babban limamin masallacin Kano Road, Sheikh Habibu Umar Mahmud, ya halarci wurin walimar, inda shi ma ya sa albarka tare da yin addu’o’i.

Walimar ta ƙayatar matuƙa, domin an ci an sha, sannan an yi zumunci. 

Haka kuma dukkan waɗanda su ka halarta sun ƙaru da nasihohin malaman su ka yi.

A zantawar sa da mujallar Fim, Maikano ya nuna murna da farin ciki game da wannan rana, ya ce, “Alhamdu lillahi rabbil alamin, alhamdu lillahi rabbil alamin, wassalatu, wassallamu ala rasulillah, annayul Mustapha, muntaƙa, murtada.

“A gaskiya babu abin da zan ce, alhamdu lillah, na yi wa Allah maɗaukakin sarki godiya da ya ba ni iko, ya ba ni zarafi na aurar da wannan ‘ya tawa. Ina yi masu fatan alkhairi, ina yi masu fatan zuri’a ɗayyiba, ina masu fatan zaman lafiya duniya da lahira, ina masu fatan su kasance tare a duniya, tare a cikin Aljannar Firdausi. Mu ma Allah ya ba mu wannan nasara.

“Na biyu kuma, dukkan waɗanda su ka zo wannan biki, da waɗanda su ka taimaka a wannan biki da dukkan waɗanda su ka yi addu’a a wannan biki, Allah ina roƙon ka da sunayen ka tsarkaka, waɗanda idan aka roƙe ka da su ka ke amsawa, Allah ka yi wa kowa kyayyawar sakayya, alfarmar Annabi Muhammad (s.a.w).”

Sheikh Tukur Adam na jawabi, yayin da Sheikh Haruna Musa ke zaune ya na sauraren jawabin sa

Haka kuma uban amaryar ya shaida wa wakilin mu cewa shi ya fi ba addini da malamai muhummanci a irin wannan al’amari. 

An tashi daga walimar da misalin ƙarfe 3:30 na yamma.

‘Yan fim da su ka halarci ɗaurin auren da walimar sun haɗa da Alhaji Magaji Sulaiman (Sulson), Nura MC, Ibrahim Daddy, Hamisu Bawasa, Harith Maigula, Ɗanladiyo Mai Atamfa, Hussaini Hassan da Dikko Yakubu.

Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba, amin.

Sheikh Tukur Adam da Alhaji Abdullahi Maikano Usman bayan an gama walima
Daga hagu: Nura MC, Ibrahim Daddy, Harith Maigula da Ɗanladiyo Mai Atamfa a wurin walimar

Loading

Previous Post

Ayyukan ta’addanci da kauce wa gaskiya da ake yi: Tura ta kai bango!

Next Post

Falke ka san hanya: Yadda Gwamna Namadi ya ɗau saitin bunƙasa Jigawa a cikin kwana 100

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Gwamna Umar Namadi Ɗanmoɗi

Falke ka san hanya: Yadda Gwamna Namadi ya ɗau saitin bunƙasa Jigawa a cikin kwana 100

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!