• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

‘Yan sanda sun kama Imam Abdullahi Indabawa saboda yaɗa kalaman ɓatanci a kan jarumin Kannywood

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
November 10, 2022
in Labarai
0
Indabawa (a hagu) da Abdul'aziz

Indabawa (a hagu) da Abdul'aziz

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

‘YAN sanda a Kano sun kama wani matashi mai suna Imam Abdullahi Indabawa bisa zargin yaɗa kalaman ɓata suna tare da neman wasu kuɗaɗe daga hannun Abdul’aziz Shu’aibu, wanda aka fi sani da Malam Ali na cikin shirin ‘Kwana Casa’in’.

Ana tuhumar Indabawa da yi masa barazanar ci gaba da ɓata masa suna idan har bai biya shi wasu kuɗaɗe ba. 

Hakan na ƙunshe cikin wani jawabi da kakakin rundunar ‘yan sanda ta Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya yi a yammacin shekaranjiya Talata, a hedikawatar ‘yan sanda ta jihar da ke Bompai, Kano. 

Mujallar Fim ta ruwaito cewa wanda ake zargin ya amsa laifin sa a gaban lauyan sa, amma ya roƙi a yi masa afuwa bisa abubuwan da ya aikata na kuskure. 

Ya yi nuni da cewa shi mai wa’azi ne wanda ya samu zamiya yayin wa’azin sa, har ta kai shi ga wallafa rubutun da ya taɓa mutunci da ƙima ta jarumin na Kannywood. 

A nasa ɓangaren, mai ƙarar, wato Abdulaziz Shu’aibu, ya koka matuƙa da yadda matashin ya cutar da shi da rubutun da ya wallafa.

Ya ƙara da cewa Indabawa ya nemi ya ba shi kuɗi don ya dakatar da yaɗuwar wannan rubutu na cin mutunci da ya ke yi masa, tare da yi masa barazanar ci gaba da yaɗa wasu rubuce-rubucen a wasu kafafen muddin bai ba shi kuɗi ba. 

Tuni dai ‘yan sanda sun kammala bincike kuma za su miƙa wanda ake tuhuma zuwa kotu.

Shi dai Imam Aliyu Indabawa, shi ne wanda tsohon shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Arewa (AFMAN), Alhaji Hamisu Lamiɗo Iyan-Tama, ya taɓa kaiwa kotu kan wani rubutu da ya yi a Facebook a kan ‘yan fim, ya na mai iƙirarin cewa su na ɓata tarbiyyar mutane, don haka bai kamata ‘yan siyasa su yi masu kyautar alheri ba.

Mujallar Fim ta labarta maku a farkon Satumba 2022 cewa sakamakon rubutun nasa, Iyan-Tama, wanda fitaccen jarumi ne kuma mai shirya finafinai, ya shigar da ƙara a Babbar Kotun Jihar Kano da ke garin Kano a kan zargin ya ɓata wa ‘yan fim suna.

Loading

Tags: 'yan sandaAbdul'aziz Shu'aibiAbdullahi Haruna KiyawaAFMANBompaiɓata sunaɓatanciHamisu Iyan-TamaImam Hamisu IndabawaKanokotuKwana Casa'in
Previous Post

Zaɓen 2023: Ba za mu take umarnin kotu ba – INEC

Next Post

Walima: Nihal ‘yar Fauziyya Maikyau ta cika shekara 6 a duniya

Related Posts

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry
Labarai

Furodusan Kannywood, Abubakar Galadima ya zama jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry

June 15, 2025
Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
Next Post
Nihal da mahaifiyar ta tare da kek ɗin ta

Walima: Nihal 'yar Fauziyya Maikyau ta cika shekara 6 a duniya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!