• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Za a ƙaddamar da littafin salatin Annabi a ranar Asabar a Kano

by DAGA WAKILIN MU
February 17, 2021
in Marubuta
0
Za a ƙaddamar da littafin salatin Annabi a ranar Asabar a Kano
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A RANAR Asabar mai zuwa, 20 ga Fabrairu, 2021, za a ƙaddamar da wani littafi da aka wallafa a kan salatin Annabi Muhammadu (SAW) a Kano.


Littafin, mai taken ‘Salatin Annabi Muhammadu Sallallahu Alaihi Wa Sallam: Matsayinsa Da Fa’idojinsa Da Sigoginsa’, wata marubuciya mai suna Hajiya Hajara Muhammad Kabir ce ta wallafa shi.


Ɗan kwamitin yaɗa labarai na shirya taron, Malam Ibrahim Sheme, ya bayyana cewa za a ƙaddamar da shi ne a fadar Mai Martaba Sarkin Kano da ƙarfe 10 na safe.


A cikin takardar sanarwa ga manema labarai, Sheme ya ce manyan baƙi daga sassa daban-daban na ƙasar nan ne za su halarta a ƙarƙashin jagorancin uban taron, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, yayin da Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, shi ne mai gayyata.

Ya ƙara da cewa Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje (Khadimul Islam), zai kasance babban baƙo na musamman.


Shugaban taron shi ne tsohon gwamnan Kano kuma Sardaunan Kano, Sanata Ibrahim Shekarau.


Sheme ya ce masu ƙaddamarwa su ne shahararrun ‘yan kasuwar nan, Alhaji Aminu Ɗantata, Alhaji Aliko Ɗangote, Alhaji Abdulsamad Isyaka Rabi’u da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar.


Sanarwar ta ƙara da cewa Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau na Jami’ar Bayero, Kano, shi ne zai yi bitar littafin a wajen taron.

Bugu da ƙari, ya ce da yake ana yaƙi da annobar korona ne yanzu, masu shirya taron sun tsara wajen taron yadda za a kiyaye dukkan ƙa’idojin da hukuma ta gindaya na hana kamuwa da cutar.


Marubuciyar littafin, Hajiya Hajara Muhammad Kabir, ‘yar asalin Kano ce wadda ta samu digirin farko a fannin nazarin Hausa daga Jami’ar Bayero, Kano.
Haka kuma ita ce mawallafiyar mujallar nan mai suna ‘Goshi: The Fortuna Magazine’.


Littattafan da ta wallafa sun haɗa da ‘Northern Women Development: A Focus on Women in Northern Nigeria’, wanda aka buga a cikin 2010.


A kan manufar wannan sabon littafin nata mai shafi sama da 175 da za a ƙaddamar, Hajiya Hajara ta bayyana cewa ta rubuta shi ne domin ta zaburar da al’ummar Musulmi baki ɗaya su san fa’idoji da sigogin salatin Annabi kuma su yi riƙo da shi.

Previous Post

Mutane sun turo mana roƙo guda 9,777 na mu ƙara yawan rumfunan zaɓe – INEC

Next Post

Mutum 5,000 za su sa ido kan raba kuɗin tallafin ‘N-Power’ da sauran su

Related Posts

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 
Marubuta

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 

January 1, 2025
Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 31, 2024
‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 20, 2024
Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai

November 30, 2024
Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau
Marubuta

Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau

November 27, 2024
Ƙungiyar matasa da mata za ta naɗa Ado Gidan Dabino Sarkin Mawallafan Arewa
Marubuta

Gasar rubutu: Hukumar Tace Finafinai ta bayyana gwaraza 50 na zagayen farko

November 24, 2024
Next Post
Mutum 5,000 za su sa ido kan raba kuɗin tallafin ‘N-Power’ da sauran su

Mutum 5,000 za su sa ido kan raba kuɗin tallafin 'N-Power' da sauran su

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!