• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 16, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Za a ƙaddamar da sabon bugu na littafin tarihin Daular Usmaniyya a ranar Talata

by DAGA IRO MAMMAN
November 22, 2021
in Marubuta
0
Za a ƙaddamar da sabon bugu na littafin tarihin Daular Usmaniyya a ranar Talata
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A RANAR Talata, 23 ga Nuwamba, 2021, za a yi taron ƙaddamar da sabon bugu na wani sanannen littafin tarihin Daular Usmaniyya a garin Abuja.

Kamfanin Premium Times Books ne ya ɗauki nauyin fito da bugun Nijeriya na littafin mai suna ‘The Sokoto Caliphate’.

A sanarwar da mujallar Fim ta gani, masu shirya taron sun ce a Cibiyar Tunawa da Shehu Musa Yar’Adua da ke Abuja za a yi taron ƙaddamarwar, kuma Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmed Nuhu Bamali, shi ne zai shugabanci taron.

Akwai ɗimbin manyan Nijeriya da aka gayyato. Sun haɗa da Ministan Matasa da Wasanni, Mista Sunday Dare, wanda zai zama babban baƙo na musamman, yayin da Alhaji Nasiru Danu, shugaban kamfanin Casiva Limited, zai zama babban mai ƙaddamarwa.

Babban Editan jaridar’21st Century Chronicle’, Malam Mahmud Jega, shi ne zai gabatar da sharhi kan littafin, inda daga nan wasu zaɓaɓɓun mutane za su yi tattaunawa kan littafin a kan maudu’in muhimmancin tarihin Daular Usmaniyya ga Nijeriyar mu ta yau (wato “The Relevance of the History of the Sokoto Caliphate to Present-day Nigeria.”

Waɗanda aka zaɓa su yi tattaunawar a kan jigon su ne Farfesa Mukhtar Umar Bunza, Kwamishinan Ilimin Gaba da Firamare na Jihar Kebbi; da Farfesa Mohammed Junaid na Tsangayar Ilimi ta Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sokoto; da kuma shi Malam Jega.

Babban Janar Manajan Hulɗa da Jama’a na kamfanin man fetur na Nijeriya, wato NNPC, Mista Ohi Alegbe, shi ne mai tsawatarwa a lokacin tattaunawar. Hasali ma dai shi ne zai yi aikin sanƙira a taron.

Farfesa Murray Last

Tun a ranar 1 ga Nuwamba ne dai aka gudanar da ɗan ƙaramin bikin ƙaddamar da littafin a Sakkwato a wani sashe na bikin murnar zagayowar ranar da aka naɗa Alhaji Abubakar Sa’ad a matsayin Sarkin Musulmi na 13.

Shi dai wannan littafi mai taken ‘The Sokoto Caliphate’, kamfanin Longmans ne ya fara buga shi a tun a cikin 1967, sakamakon zurfin bincike da Farfesa Denis Murray Last ya yi a lokacin da ya ke ɗalibin digiri na uku (PhD) a Jami’ar Badun.

Jigon littafin shi ne Daular Usmaniyya da aka kafa a ƙarni na 19 miladiyya a ƙarƙashin Mujaddadi Shehu Usmanu Ɗanfodiyo.

An bayyana cewa a lokacin da ta ke kan ganiyar ta, wannan daula ta malala tun daga ƙasar Kamaru ta yau, ta yi yamma zuwa Burkina Faso, sannan daga arewa zuwa gabas tun daga Agadas har zuwa Ilori.

Turawan mulkin mallaka, musamman ‘yan Birtaniyya da Faransa, sun riƙa kiran yankin da sunan Daular Fulani.

Loading

Tags: book launchcolonialismMahmud JegaMurry LastNasiru DanuNNPCSarkin Zazzau Ahmed Nuhu BamalliShehu Musa Yar'Adua CentreShehu Usmanu DanfodioSokoto CaliphateSunday Dare
Previous Post

An yi wa babban ɗan Sarkin Kano da ɗiyar Ummarun Kwabo baiko a Sakkwato

Next Post

Aishatu Musa Dalil, ‘yar shekara 18, ta lashe gasar rubutu ta ‘Hikayata’ ta 2021

Related Posts

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 
Marubuta

Gasar rubutu: Ba a taɓa ba marubutan Hausa dama irin wannan ba – Balannaji 

January 1, 2025
Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Zubairu Balannaji ya zama gwarzon gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 31, 2024
‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

‘Dakan ɗaka…’: Kanawa sun lashe gasar rubutu ta Hukumar Tace Finafinai

December 20, 2024
Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai
Marubuta

Mutane 15 sun yi nasarar zuwa zagayen kusa da na ƙarshe a gasar rubutu na Hukumar Tace Finafinai

November 30, 2024
Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau
Marubuta

Tsakanin matan aure biyu da budurwa ɗaya za a san gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024 a yau

November 27, 2024
Ƙungiyar matasa da mata za ta naɗa Ado Gidan Dabino Sarkin Mawallafan Arewa
Marubuta

Gasar rubutu: Hukumar Tace Finafinai ta bayyana gwaraza 50 na zagayen farko

November 24, 2024
Next Post
Aishatu Musa Dalil, gwarzuwar gasar 'Hikayata' ta bana, riƙe da kambin ta a zaure taron karramawar

Aishatu Musa Dalil, 'yar shekara 18, ta lashe gasar rubutu ta 'Hikayata' ta 2021

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!