• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Za mu tsarkake Kannywood, inji sabon shugaban ƙungiyar furodusoshin Arewa Sani Sule Katsina

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
January 24, 2022
in Labarai
0
Alhaji Sani Sule Katsina riƙe da satifiket ɗin sa na zama sabon shugaban AFMAN

Alhaji Sani Sule Katsina riƙe da satifiket ɗin sa na zama sabon shugaban AFMAN

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SABON shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Arewa (Arewa Film Makers Association of Nigeria, AFMAN), Alhaji Sani Sule Katsina, ya bayyana cewa babban ƙudirin da ke gaban sa shi ne tsarkake masana’antar finafinai ta Kannywood, kuma gyaran zai fara ne daga su kan su shugabannin harkar.

Ya ce, “Za mu tsarkake kan mu, mu tsarkake tafiyar gaba ɗaya don a samu tsafta a cikin ta in Allah ya yarda.”

An zaɓi Sani Katsina ɗin ne a wajen babban taron ƙungiyar na ƙasa, karon farko, wanda aka gudanar a Kano a yammacin ranar Lahadi, 23 ga Janairu, 2022.

A taron, an zaɓi shugabannin a muƙamai 16 da za su jagoranci ƙungiyar wadda ta haɗa jihohin Arewa 19.

Ana rantsar da sababbin shugabannin

Bayan an kammala taron haɗi da gudanar da zaɓuɓɓuka, kwamitin shirya zaɓen, a ƙarƙashin jagorancin Mika’ilu Isa bin Hassan (Gidigo), ya gabatar da sakamakon abin da su ka tattara na zaɓen inda aka sanar da cewa Alhaji Sani Sule Katsina ne aka zaɓa a matsayin shugaban ƙungiyar.

Shugabannin da aka zaɓa ɗin dai su ne:

1. Sani Sule Katsina – Shugaba

2. Rasheeda Adamu Maisa’a daga Jihar Kano – Mataimakiyar Shugaba ta 1

3. Wassh Waziri Hong daga Kaduna –  Mataimakin Shugaba na 2

4. Habibu Baffa Jalingo daga Taraba – Mataimakin Shugaba na 3

5. Salisu Muhammad Officer daga Kano – Babban Sakatare 

6. Kwamared M.B. Mukhtar daga Neja – Ma’aji

7. Jamilu Ahmad Yakasai daga Kano – Sakataren Kuɗi 

8. Amina Adamu daga Kano – Mataimakiyar Sakatare 

9. Nasiru B.A. Hassan daga Sokoto – Sakataren Tsare-tsare 

10. Audu Boda daga Katsina – Mataimakin Sakataren Kuɗi 

11. Muhammad Mukhtar Daneji daga Kano – Jami’in Hulɗa da Jama’a na 1

12. Yahaya B. Abubakar daga Kebbi – Jami’in Hulɗa da Jama’a na 2 

13. Jamila Umar Nagudu daga Bauchi – Mataimakiyar Sakataren Tsare-tsare

14. Hadizan Saima daga Kano – Jami’ar Walwala 

15. Hamza Jibrin – Mai Binciken Kuɗi na 1 

16. Halima Muhammad – Mai Binciken Kuɗi ta 2

Shugabannin tare da Afakallahu jim kaɗan bayan an rantsar da su

Jim ƙaɗan bayan kammala karɓar rantsuwar kama aiki ne sabon shugaban ƙungiyar ya yi wa mujallar Fim ƙarin haske kan wannan nauyi da aka ɗora masa inda ya fara da gode wa Allah tare da faɗin, ”Na yi matuƙar farin ciki da wannan nauyi da Allah ya ɗora mani kuma ina roƙon Ubangiji Allah ya ba ni damar da zan sauke kuma in yi abin da ya kamata da mutanen da su ka dace.”

Alhaji Sani ya kuma bayyana ƙudirin da ya ke son cimmawa a wannan ƙungiya domin samun cigaba ta kowane fanni, ya ce: “Akwai ƙudire-ƙudire saboda na san matsalolin da ke cikin wannan masana’anta gaba ɗaya tunda na daɗe a cikin ta kuma ina shugabanci a cikin ta kuma na san yadda za mu fuskance su.

“Ɗaya daga cikin matsalolin mu shi ne rashin ƙofa ta shigowa da ta fita kuma da rashin katanga inda wasu sai su yi wani abu ake zaton mu ne. To in Allah ya yarda za mu yi abin da za mu gyara kuma za mu ba wa jama’a mamaki. 

“Za mu tsarkake kan mu, mu tsarkake tafiyar gaba ɗaya don a samu tsafta a cikin ta in Allah ya yarda.”

Haka kuma ya ce maganar ƙalubale da man ya riga ya san da su kuma sun shirya tsaf don ganin an fuskance su tare da kawo ƙarshen su.

Afakallahu ya na jawabi a taron

Taron dai ya samu halartar wasu daga cikin dattawan Kannywood, tare da shugaban Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Alhaji Isma’il Na’abba (Afakallah).

Loading

Tags: Arewa Film Makers Associationhausa filmsIsma'il Na'abba Afakallah.Sani Sule Katsinazaɓe
Previous Post

Wasiƙa zuwa ga Malam Abdallah Gadon-Ƙaya

Next Post

Jarumar Kannywood kuma mawaƙiya Hauwa Rafin Guza za ta yi aure ranar Asabar

Related Posts

AFMAN ta taya Sarari murnar samun damar halartar taron baje-kolin finafinan Nijeriya a Toronto da fim ɗin ‘Kakanda’
Labarai

AFMAN ta taya Sarari murnar samun damar halartar taron baje-kolin finafinan Nijeriya a Toronto da fim ɗin ‘Kakanda’

June 16, 2025
Naɗa ni jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry Powder da aka yi zai amfani Kannywood baki ɗaya, inji furodusa Abubakar Galadima
Labarai

Naɗa ni jakaden garin sinadarin girki na Zahir Spice Curry Powder da aka yi zai amfani Kannywood baki ɗaya, inji furodusa Abubakar Galadima

June 15, 2025
Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
Next Post
Hauwa'u Abubakar da Lawal Habeeb

Jarumar Kannywood kuma mawaƙiya Hauwa Rafin Guza za ta yi aure ranar Asabar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!