TARON Haɗin Gwiwar Ƙasashen Larabawa da sauran ƙasashen Musulmai ya yi tir tare da nuna rashin amincewa da hare-haren da sojojin Isra’ila ke ci gaba da kaiwa a Zirin Gaza.
Taron, wanda aka gudanar a ranar Asabar, 11 ga Nuwamba, ya bayyana cewa abin da sojojin Isra’ila su ka yi laifin tsallake ƙa’idoji da sharuɗɗan yaƙi ne, kuma dabbanci ne kan Falasɗinawa fararen hula.
Ministan Yaɗa Labarai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa da Jami’in Yaɗa Labarai na ministan, Malam Rabi’u Ibrahim, ya fitar.
Idris, wanda ya na cikin tawagar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a wurin taron, ya ƙara da cewa kuma an yi kira da a gaggauta gudanar da gagarumin taron duniya, inda za a bijiro da hanyoyin tabbatar da wanzuwar zaman lafiya a yankin Falasɗinu.
Sanarwar bayan taron da wanda shugabannin ƙasashen Ƙungiyar OIC da na Majalisar Ƙasashen Larabawa su ka halarta, an yi kira da a gaggauta tsagaita dukkan hare-haren da sojojin Isra’ila ke kaiwa a Gaza.
Kuma sun fito ƙarara sun ce farmakin da Isra’ila ke kaiwa kan Gaza ci gaba ne da irin mamayar da ta yi wa Falasɗinawa a 1967 a yankin da West Bank, Masallacin Ƙudus da kuma Arewacin Birnin Ƙudus.
Sannan kuma taron ya buƙaci Majalisar Ɗinkin Duniya da ta fito da ƙwaƙƙwarar matsaya a ƙarƙashin Majalisar Tsaro ta Majalisar Ɗinkin Duniya wadda za ta tilasta daina duk wani nau’i da salo na gallazawa da Isra’ila ke yi wa Falasɗinawa.
Haka nan kuma wannan taro ya nemi Isra’ila ta kawo ƙarshen mamayar da ta ke yi a yankin, domin ya karya ƙa’ida da iyakokin da dokokin ƙasa da ƙasa su ka shar’anta.
Sun ce musamman farmakin ya saɓa wa Ƙudirin Majalisar Ɗinkin Duniya mai lamba AES-101.25 na ranar 26 ga Oktoba, 2013.
A wurin taron, shugabannin sun yi kakkausan kira ga Majalisar Tsaro ta Majalisar Ɗinkin Duniya cewa “ta gaggauta yin Allah-wadai da dabbacin da sojojin Isra’ila ke kan yi na ruguza asibitoci a Zirin Gaza. Kuma ta yi tir da hana a shigar wa Falasɗinawa da magunguna, abinci, fetur da katse wutar lantarkin da mahukuntan Isra’ila ɗin su ka yi a Zirin Gaza.”

An zartas da cewa matuƙar Majalisar Ɗinkin Duniya ta ƙi yin tir da dabbancin da sojojin Isra’ila ke aikatawa a Zirin Gaza, to tamkar ta halasta mummunan kisan da ake wa fararen hula ne da su ka ƙunshi ƙananan yara, dattawa, mata da kuma ruguza Gaza da ake kan yi.
Sun ce ya zama wajibi Isra’ila ta ɗage takunkumin datse Zirin Gaza da ta yi tsawon shekaru masu yawa.
Sannan kuma taron ya yi tir dangane da yadda wasu ƙasashe su ka riƙa taimaka wa Isra’ila da muggan makaman da ta ke amfani da su ta na kisan gilla kan Falasɗinawa, tare da ruguza masu gidaje, asibitoci, makarantu, masallatai, coci-coci da sauran wuraren more rayuwa.
