AN bayyana sabuwar Ƙungiyar Mawaƙa Mata na Kannywood da cewa wani gungun ne na mutanen da ba su da wata manufa sai son zuciya da son kan su, don haka babu inda za su je.
Ɗaya daga cikin sanannun mawaƙa mata, Fa’iza Badawa, ita ce ta bayyana hakan a lokacin tattaunawar ta da mujallar Fim dangane da ƙungiyar.
Idan kun tuna, a shekaranjiya Litinin mujallar Fim ta ba ku labarin kafa ƙungiyar, inda har mu ka yi hira da shahararriyar mawaƙiya Maryam A. Baba kan manufofin kafa ƙungiyar.
A raddin da ta yi, Hajiya Fa’iza ta ce: “Tun asali ma ba su su ka kafa ƙungiyar ba, ni na kafa ta. Don in za ka iya tunawa a wata hira da mujallar Fim ta yi da ni a baya, na faɗa maka na kafa sabuwar ƙungiya kuma ina jawo mawaƙa domin mu taru mu haɗa kai domin mu taimaki juna.”
Ta ƙara da cewa: “Da na kafa ƙungiyar, sai na kirawo su a waya na ce na kafa ƙungiya. To, bayan mun zo an zauna za a kafa ƙungiya, sai na ce to ya na da kyau a raba muƙamai kafin a gama shirye-shirye. Da su ka amince sai na ce to ina son a bai wa Murja Baba shugaba, don haka sai mu ka samar da shugabanci kafin a kammala tsarin da za a yi.
“To, bayan mun yi haka sai mu ka samu aiki a Gombe wanda mu ka yi wa Gwamnan Gombe. Tun da aka je aka samo kuɗi naira miliyan tara, tun daga nan sai su ka fara canzawa. Domin da aka samo kuɗin ya kamata a zo Kano a zauna da ni da na kafa ƙungiya da sauran ‘yan cikin ta, a zo a san yadda za a raba kuɗi a fitar da kuɗin aikin da aka yi. To tun daga can sai su ka raba kuɗi.
“Ni ban je Gombe ba, amma a can su ka fara raba kuɗi a junan su, su ba wanda su ka ga ya dace, su hana wanda su ka ga bai dace ba.
“Sannan sai su ka rinƙa bai wa ƙananan mawaƙa kuɗi kaɗan, kuma wannan bai kamata ba tun mawaƙiya ta na ƙarama ki ba ta kuɗi kaɗan, saboda ai tare ku ka je, amma ya za a yi ki ɗauki kuɗin da ya linka nata sau uku? Wannan bai kamata ba in dai taimakon juna za a yi, sai a zo a yi waɗanda su ka yi waƙa kuɗin su daban, waɗanda ba su yi waƙa ba kuɗin su daban.
“Amma sai su ka ɗauka hakan ba zai yiwu ba saboda su manya ne.
“Sannan duk wanda ya bi ta hanyar su aka tafi da shi, sai sun linka masa kuɗi. Kuma ba haka ake yin rayuwa ba. In dai ka ce ka na son ka kafa mutum da ya zama mutum, to ba za ka kafa ƙungiya don ka cuce shi ba. Ya za ka kafa ƙungiya don ka tallafa wa na ƙasa sannan ka zo ka na cutar sa ka na danne masa haƙƙi? Ai ba a yin haka a rayuwa.
“Shi ya sa na faɗa maka, ƙungiyar babu inda za ta je, in dai da zalunci a cikin ta. Don ka ga ni na kafa ƙungiya, kuma kowacce mawaƙiya ni na kira ta na ce ta zo a haɗu a kafa ƙungiya. Don haka ƙungiya ta ce, kuma na fita.
“Don haka babu inda za ta je. Tunda akwai zalunci a cikin ta sai ta rushe wallahi.”