WASU ɗalibai masu nazarin harshen Hausa a Jami’ar Bayero, Kano, ‘yan asalin ƙasar Sin (Chaina), sun kai ziyara ga mawaƙi Aminu Ladan Abubakar (Ala) a ofishin sa da ke Titin Gidan Zu a Kano.
Sun kai ziyarar a ranar Juma’a, 1 ga Disamba, 2023 bisa jagorancin ɗaya daga cikin malaman su, Malam Kamilu Ɗahiru Gwammaja.
A jawabin sa a taron, Malam Kamilu ya faɗi dalilin su na kai ziyarar, ya ce, “Waɗannan ɗaliban mu ne a Jami’ar Bayero da su ka zo daga Jami’ar Beijing da kuma Jami’ar Tenjan daga ƙasar Sin inda su ke nazari a kan harshen Hausa, mu ka zo da su domin su ga Aminu Ala shi ma ya gan su a matsayin sa na mawaƙin Hausa da su ke da sha’awar haɗuwa da shi.”

Ya ƙara da cewa, “Babbar manufar wannan ziyara ita ce haɗuwa tare da ji daga shi Aminu Ala na abin da ya shafi tarihin rayuwar sa da yadda ya ke waƙoƙin sa da kuma irin nau’in mutanen da ya ke yi wa waƙa.
“Don haka Aminu Ala ina gabatar maka da baƙin ka da su ka zo domin su ziyarce ka a matsayin ka na mawaƙin da su ke son haɗuwa da shi.”
Bayan ya kammala gabatarwar, kowanne daga cikin ɗaliban ya tashi ya gabatar da kan sa da kuma sunan sa, tare da jin daɗin sa na haɗuwa da shahararren mawaƙin.

A cewar su, su na sauraron waƙar Ala a ƙasar Sin a matsayin su na masu nazarin Hausa, kuma waƙoƙin sa su na ƙayatar da su.
A lokacin da ya ke yi masu bayani, Ala ya nuna farin cikin sa da zuwan su tare da yi masu bayani a taƙaice kan tarihin sa da yadda ya ke gudanar da waƙoƙin sa, tun farkon fara waƙar sa zuwa yanzu.

Baƙin sun nuna gamsuwa da farin ciki kan yadda aka karrama su, su ka yi fatan zumuncin su zai ɗore tare da fatan za a sake karɓar su da hannu biyu-biyu a duk lokacin da su ka samu damar dawowa.

![]()







