• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, June 30, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gasar ‘Ƙidaya Challenge’: Yadda ‘yan Arewa su ka juya wa mawaƙi Rarara baya

by DAGA EL-ZAHARADDEEN UMAR
October 22, 2023
in Mawaƙa
0
Alhaji Dauda Abdullahi Kahutu (Rarara)

Alhaji Dauda Abdullahi Kahutu (Rarara)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

YANZU haka dai alamu na nuni da cewa gasar rawa ko rawa da fitaccen mawaƙin siyasar nan Dauda Adamu Abdullahi (Rarara) ya saba sanyawa musamman ga mutane masu ta’amuli da soshiyal midiya ta samu cikas.

A wannan karon, kamar yadda ya saba, Rarara ya sanya gasa ne a kan sabuwar waƙar sa da ya yi ta yin kira ga al’umma a kan batun ƙidaya da Gwamnatin Tarayya ta shirya, manufa dai ya na son wannan saƙo ya shiga lungu da saƙo na Nijeriya, musamman na Arewa. 

Mawaƙin ya na ware wasu kyaututtuka da ake raba wa waɗanda su ka yi zarra a gasar, kamar yadda ya yi a gasar waƙar ‘Baba Buhari Ɗoɗar’ da waƙar Sha’aban Sharaɗa.

A cikin wannan makon da mu ke ciki babu batun da ya dabaibaye soshiyal midiya kamar wannan batu da ya kira da ‘Kidaya Challenge’. Yayin da wasu na suka, wasu kuwa na yabo, amma dai masu sukar sun fi yawa, wanda hakan ya sa wakilin mujallar Fim ya bibiyi lamarin. 

Babbar ta hannun damar mawaƙin, A’isha Ahmad Idris (Ayshatulhumairah), ita ce ta fara bada sanarwar gasar a TikTok inda ta yi dogon bayani kan shirye-shirye da tsare-tsaren yadda gasar za ta kasance da irin kyaututtukan da za a raba wa waɗanda su ka yi nasara.

Yin sanarwar ke da wuya jama’a su ka fara maida martani marar daɗi inda wasu ke cewa su yanzu ba wannan ba ce a gaban jama’ar Arewa, matsalar tsaro ita ce abin da ya fi damun su.

A wannan ɓangare kuwa, wasu na sukar gasar ne da cewa Rarara ya karɓo kwangila mai ƙarfin gaske, ya zo ya gutsura wa mutane ɗan abin da bai taka ƙara ya karya ba, don ya lura da halin ƙuncin da al’umma ke ciki.

Wasu har da yin barazana ga duk wani mai amfani da TikTok da cewa duk wanda ya yi wannan gasar kuma ya ɗora a shafin sa to a ƙaurace masa, a daina bibiyar sa baƙi ɗaya.

Ta wani ɓangaren kuma akwai masu ra’ayin komai zai faru ya daɗe bai faru ba, sai sun yi gasar tunda kuɗi za su samu, kuma su na da buƙatar kuɗi.

Aisha Ahmad Idris (Ayshatulhumairah) ta na bayyana fa’idar gasar a saƙon da ta wallafa a TikTok da Instagram

Su kuwa mutanen Rarara, bayan sun lura da cewa jama’a da dama sun juya wa wannan lamari baya kuma sun fara fusata da mawaƙin, musamman su na sukar sa da cewa ana famar kashe-kashe a Arewa amma ba a ji ya yi waƙar kira ga gwamnati da ta ɗauki mataki ba sai kawai aka ji ya na sanya gasa kamar yadda ya saba.

Ba su yi wata-wata ba wajen maida martani da faɗin cewa su dai kam, sai dai a kar tsohuwa akan daddawar ta, har ma su na kawo wata waƙa da mawaƙin da sauran mawaƙa na ƙungiyar 13×13 su ka yi a kan batun matsalar tsaro, tare da faɗin cewa ina jama’a su ke lokacin da mawaƙin ya yi wannan waƙar?

Kazalika ita ma A’ishatulhumaira da ta bada sanarwar, bayan ta lura da cewa kashi mai yawa na jama’ar da su ke sa ran cewa za su yi wannan gasa sun juya mata baya, sai ta sake fitowa a TikTok ta ƙara yin dogon bayani.

A bidiyon da ta ɗora, mai ɗauke da hoton Rarara da na Shugaban Hukumar Kidaya ta Ƙasa (NPC), Alhaji Nasir Isa Kwarra, jarumar ta Kannywood ta bayyana cewa wannan gasa babu dole, ba a ce sai mutum ya yi ba.

Ta ƙara da cewa wannan aiki na ƙidaya fa zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro a arewacin Nijeriya. 

Haƙika wannan kalami bai yi wa jama’a daɗi ba, baya ga maida martani wasu sun bi ta da ashariya a yayin da wasu kuma nasiha su ka yi mata.

Yanzu dai a iya cewa wannan gasa ta haɗu da tasgaro; duk da halin ƙuncin da al’umma ke ciki kuma su na buƙatar kuɗi amma su ka kau da kan su daga wannan gasa tare da faɗin su matsalar tsaro ta dame su ba gasa ba.

Shin ko yaya Rarara ya ji da kuma lura da wannan ce-ce-ku-ce da ake yi a kan wannan gasa?

Mujallar Fim ta tuntuɓe shi ta wayar tarho domin jin nasa ba’asi kan wannan tirka-tirka, sai dai kash! wayar sa a kashe ta ke.

Shi ma mai taimaka wa mawaƙin ta fuskar yaɗa labarai, Rabi’u Garba Gaya, bai dauki wayar da wakilin mu ya yi masa ba ko ya amsa saƙon tes da ya tura masa domin jin daga ɓangaren su har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Loading

Previous Post

Ubalen Danja da A’isha sun samu ɗan fari

Next Post

An yi taron walimar saukar Alƙur’ani ta ‘yar Abba El-Mustapha

Related Posts

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi
Mawaƙa

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi

April 19, 2025
Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala

October 28, 2024
Abin da ya sa na koma yin waƙa da kayan kiɗan gargajiya – Aminu Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa na koma yin waƙa da kayan kiɗan gargajiya – Aminu Ala

July 16, 2024
Nazarin waƙar ‘Fatima Mai Zogale’ ta Dauda Kahutu Rarara
Mawaƙa

Nazarin waƙar ‘Fatima Mai Zogale’ ta Dauda Kahutu Rarara

May 13, 2024
Waɗansu waliyyai a Nijar da Nijeriya 
Mawaƙa

Waɗansu waliyyai a Nijar da Nijeriya 

December 7, 2023
Ɗaliban Hausa ‘yan ƙasar Sin sun ziyarci mawaƙi Aminu Ala
Mawaƙa

Ɗaliban Hausa ‘yan ƙasar Sin sun ziyarci mawaƙi Aminu Ala

December 3, 2023
Next Post
Alhaji Abba El-Mustapha tare da A'isha da sauran iyalin sa a wajen taron

An yi taron walimar saukar Alƙur'ani ta 'yar Abba El-Mustapha

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!