• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, May 15, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cewar Farfesa Yakubu: INEC ta shirya wa zaɓen gwamnan Anambra na ranar Asabar

by DAGA WAKILIN MU
November 3, 2021
in Nijeriya
0
Farfesa Mahood Yakubu

Farfesa Mahood Yakubu

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa ta shirya tsaf domin gudanar da zaɓen gwamnan Jihar Anambra cikin lumana wanda za a yi a ranar Asabar mai zuwa, 6 ga Nuwamba.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a yayin da ya ke ganawa da manema labarai a ranar Talata a ofishin hukumar da ke garin Awka, babban birnin jihar.

Ya ce: “Lokacin da hukumar ta saki jadawalin ranakun da za a gudanar da zaɓen, watanni bakwai da su ka gabata, tunanin da wasu su ka yi shi ne lokacin ba zai zo ba.

“To ga shi har lokacin ya zo, saura kwana huɗu kacal su ka rage mana, kuma za mu ci gaba a hakan a matsayin mu na hukuma.” 

Yakubu ya ce hukumar ta shirya domin gudanar da zaɓe fisabillahi, kuma mai adalci da inganci.

Ya yi la’akari da cewa ƙalubale guda ɗaya kacal da hukumar ke fuskanta shi ne yadda za ta tabbatar da cewa sababbin masu zaɓe da aka yi wa rajista sun shiga zaɓen an yi tare da su.

Ya ce, “Don tabbatar da cewa sababbin masu zaɓe da aka yi wa rajista su ma sun yi zaɓe, mun yanke shawarar mu tuntuɓe su ta hanyar imel ɗin su da lambobin wayar hannun su domin mu sanar da su wuraren da za su je su karɓi katittikan su.”

Shugaban, wanda ya ce ya kai ziyara jihar ne domin ya yi jawabi ga taron da za a yi da masu ruwa da tsaki a zaɓen a ranar Laraba, ya ce taron zai ƙunshi rattaba hannu a kan yarjejeniyar zaman lafiya a tsakanin ‘yan takarar zaɓen.

Ya yi kira ga dukkan masu zaɓe da su fito a yi zaɓen da su tunda an yi duk wani shiri na tabbatar da gudanar da zaɓen a cikin lumana.

A nasa tsokacin, Kwamishinan ‘Yansanda na jihar, Mista Echeng Echeng, ya ce su ma hukumomin tsaro sun gama duk wani shiri domin zaɓen.

Echeng ya ce akwai isassun ababen hawa, kwale-kwale da helikwaftoci da za a yi amfani da su wajen sa ido a dukkan faɗin jihar. 

Ya ƙara da cewa sauran hukumomi ma sun gama nasu shirin.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa jami’an tsaro za su taƙaita zirga-zirgar jama’a daga tsakar daren ranar Juma’a, 5 ga Nuwamba, don hana shigowar ɓatagari zuwa cikin jihar.

Loading

Tags: AwkaEcheng EchengHukumar Zabe ta Kasa (INEC)Independent National Electoral CommissionINECKwamishinan 'YansandaProfessor Mahmood Yakubuzaben gwamnan Jihar Anambra
Previous Post

Attah Dabai: Ba rabo da gwani ba…

Next Post

Zaɓen Anambra: INEC ta ƙara matakan tsaro

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
INEC ta yi wa masu zaɓe 30,449 rajista a Filato

Zaɓen Anambra: INEC ta ƙara matakan tsaro

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!