ƊAN takarar shugabancin ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi wa al’ummar Jihar Gombe alƙawarin zai farfaɗo da madatsar ruwa ta Daɗin Kowa domin a riƙa samar da wutar lantarki ga ƙasa, idan har aka zaɓe shi a 2023.
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasar ya yi wannan alƙawarin ne lokacin da rundunar yaƙin neman zaɓen PDP ta dira Gombe domin ci gaba da kamfen ɗin sa.
Haka kuma ya yi alƙawarin gina dukkan titinan da su ka haɗe Jihar Gombe da Adamawaz Barno, Yobe da Bauchi.
Atiku ya ce ya tabbatar idan aka gina titinan waɗanda sun daɗe da lalacewa, harkokin kasuwanci da cinikayya a tsakanin jihohin biyar za su ƙara bunƙasa sosai.

“Mu na kuma ƙara jaddada cewa Daɗin Kowa Dam wanda dama tun asali PDP ce ta gina shi domin samar da wuta da noman rani, to idan mu ka ci zaɓe za mu sake farfaɗo da shi domin bunƙasa lantarki da noman ranin.
Ya ce: “Kuma za mu tabbatar cewa mun gina dukkan titinan da su ka haɗa Gombe, Barno, Bauchi, Yobe da Adamawa, domin inganta harkokin cinikayya.”
Wazirin na Adamawa, wanda ɗan asalin Jihar Adamawa ne, ya kwatanta kan sa da Firayim Minista Abubakar Tafawa-Balewa.
Ya ce, “Da yawa daga cikin ku ba a haife ku lokacin mulkin Abubakar Tafawa Ɓalewa ba. To a yau ga dama ta same ku ta sake samun wani Tafawa Ɓalewa ɗin idan ku ka zaɓe ni.”
Shugaban kamfen ɗin shugaban kasa na PDP, kuma Gwamnan Jihar Akwa Ibom, Udom Emmanuel, ya ce idan PDP ta yi nasara a 2023, tattalin arzikin ƙasa zai bunƙasa, sannan darajar naira ita za ta farfaɗo.