GWAMNATIN Tarayya ta bayyana cewa ba za ta tace duk wani fim da wani kamfani maras rajista ya miƙa mata domin ta duba ba.
Ta ce kamfanoni masu lasisin rarraba finafinai (distributors) kaɗai ne za a karɓi finafinan su domin tacewa.
Hukumar Tace Finafinai da Bidiyoyi ta Nijeriya (NFVCB) ita ce ta bayyana haka a cikin wata takarda da ta aika wa shugabannin ƙungiyoyin ‘yan fim masu rajista, da rassan su da kuma sauran masu ruwa da tsaki a harkar shirya finafinai a Nijeriya.
Mataimakin shugaban ma’aikata na Babban Sakataren hukumar, Mista Ogbonna Onwumere, shi ne ya rattaba hannu a kan takardar mai ɗauke da kwanan wata 28 ga Yuni, 2022.
A cikin wasiƙar, wadda aka miƙa wa mujallar Fim kwafe ɗin ta, hukumar ta ce ta lura da cewa akwai waɗansu kamfanonin rarraba finafinai waɗanda lisisin su ya ƙare amma “har yanzu su na yawo su na faɗin cewa wai su ma kamfanonin rarraba finafinai ne.”

Hukumar ta ce domin magance wannan matsalar, ta kammala rubuta jerin dukkan kamfanonin masu rarraba finafinai waɗanda ke da cikakkiyar rajista da ita daga ranar 27 ga Yuni, 2022.
Ta ce: “Wannan ya yi daidai da Sashe na VI na dokar hukumar, wato Act 1993 CAP N40 LFN 2004 da Dokokin 2008, wadda ta ce ‘ba a amince wa duk wani mutum ya yi harkar rarraba ko nuna finafinai ko bidiyoyi ba har sai ya na da lasisi wanda wannan Hukuma ta ba shi a ƙarƙashin wannan Dokar’.”
Hukumar ta yi kira ga masu shirya finafinai da su yi hulɗa da kamfanonin rarraba finafinai waɗanda ke cikin jerin sunayen da ke wajen ta domin su kauce wa ƙorafin ɓata lokaci wajen ba su satifiket ɗin tace fim ɗin su.
Ta ce: “Ana shawartar masu shirya finafinai waɗanda su ka miƙa finafinan su ta hanyar kamfanonin da ba su cikin wannan jerin sunayen da su rubuto takarda ga Hukumar ta neman sauya kamfanin rarraba fim, idan ba haka ba kuwa Hukumar ba za ta tace fim ɗin su ba.”