TSOHUWAR shugabar Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), reshen Jihar Kaduna, Hajiya Fatima Ibrahim Ahmad (Lamaj), ta bayyana cewa ba ta ja baya da harkar fim ba, ta dai koma gefe ne don ganin irin abubuwan da ke wakana yanzu a masana’antar.
Lamaj ta yi wannan bayani ne yayin da ta ke tattaunawa da mujallar Fim, bayan an daina jin ɗuriyar ta gaba ɗaya a kan harkar masana’antar Kannywood.
Ta ci gaba da cewa, “Amma alhamdu lillahi, akwai fim da na ke so na yi kwanan nan in-sha Allahu nan da bayan Sallah. Fim ɗin kuma a kan rayuwar ‘yan mata ne, a kan haka zan yi fim ɗin, za ka ga fastocin fim ɗin na yawo a soshiyal midiya. Aƙalla mata kusan goma ne cikin fim ɗin, ba a maganar maza, amma akwai mazan sai dai ba su da yawa, saboda labarin a kan mace ne; ‘Gidan Zeenat’.
“Abubuwan da ake tafkawa a ‘Gidan Zeenat’, shi mutane za su saurara su gani in fim ɗin ya fito. Don ko yanzu da mu ke magana ina Legas, na je magana a kan wanda zai yi min dillancin fim ɗin.
“Haka kuma na je na zauna da wasu masu gidajen talbijin don ganin na kai masu fim ɗin. Sannan kuma akwai wani sabon gidan talbijin da za a buɗe nan da Satumba, na zauna da su, mun yi yarjejeniya da su, har an saka hannu zan ba su fim ɗin Turanci guda goma, amma zai zama matan mu da mazan mu Hausawa ne za su kasance a ciki, don su na so su ga ya aikin su ya ke a kan aikin fim ɗin Turanci. Don haka mun gama magana zan yi masu finafinai goma in Allah ya yarda.”

Da mu ka tambaye ta abin da za ta ce game da mulkin MOPPAN na Jihar Kaduna a yanzu, sai ta amsa da cewa, “Ni yanzu babu abin da zan ce a kan mulkin MOPPAN na yanzu, saboda ni ba shiga cikin su na ke yi ba. Kwanaki dai sun yi ‘workshop’ da ‘National Film and Video Censors Board’, sun gayyace ni, amma Allah bai ba ni ikon zuwa ba.
“Amma kuma a taron ‘National Exco’ da aka yi a Kano, mun haɗu da shi ciyaman na MOPPAN reshen Jihar Kaduna.
“Ni yanzu na zarce wa Kaduna, tunda ina ‘national’ ne. To wanda ke sama kuma ya za a yi ta waiwayi jiha? Yanzu jiha ba hurumi na ba ne, akwai wanda hurumin su ne jiha, to su ne mu ka koma gefe, mu ka zura wa ido mu ga me za su yi mana.
“Ga masu zaɓe, waɗanda su ka zaɓe mu baki ɗaya, sun san wacece Lamaj. Kuma sun san su waye su ke mulki yanzu. Lokacin da ni na ke shugabantar Kaduna, sun san me da me na yi a zamani na. Tunda na yi finafinai biyar zuwa shida. Alhamdu lillahi, yanzu ga zamani, Allah ya ba Kaduna zamani daidai da abin da ta ke so. Abin da Kaduna su ka zaɓa, shi Allah ya ba su. Ni kuma da su ka ce ni mace ce bai kamata a ce mace ta mulke su ba, alhamdu lillahi, kowa mace ta haife shi, kuma namiji ba zai iya auren namiji ɗan’uwan sa ba, dole sai dai mace zai aura. Haka kuma namiji bai da zaɓi in Allah ya ba shi zuri’a ya ce namiji ya ke so.
“Don haka mace ta na gaba da komai, tunda Allah ma sai da ya ambaci mahaifiya sau uku, sannan ya ambaci mahaifi.
“Yanzu ni babu abin da zan ce wa industiri sai godiya, saboda ni yanzu gaba na yi. Mutanen da na ke mu’amala da su yanzu lokacin da na ke ‘chairperson’ na Kaduna State MOPPAN, wallahi ban san su ba, bari na jiha ya ƙara buɗe min ido. Tunda yanzu za ka ga an gayyace ni ‘film festival’, an saka ni a kwamiti na ‘film festival’, ka ko san cewa ai cigaba ne.
“Duk wanda ya riga ya yi gaba, ba ya waiwayar baya. Saboda ko yanzu aka ce Lamaj dawo ga Kaduna an ba ki, ba sai kin sayi fom ba, zan roƙe su in ce su yi haƙuri su ba waɗanda su ke so.
“Yanzu fim ɗin da zan yi, akwai ‘yar Abuja, akwai ‘yar Bauchi, akwai ‘yan Kaduna, akwai ‘yan Kano, haka na cakuɗa su. Kuma tunda fim ne mai dogon zango, za a riƙa buɗawa ana ɗauko na wasu jihohin ana sakawa a ciki.
“A matsayi na na ‘national exco’, babu abin da zan ce, godiya na ke yi wa Allah da sakayyar da ya yi min da Kaduna su ka ce ba su yi na, kuma ‘national’ su ka ce su na yi na, don haka me zan cewa MOPPAN, sai hamdala.
“Ina godiya ga kowa da kowa, ina kuma yi maka fatan alkhairi Abba.”