• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, July 21, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Cewar gwamnatin Kano: Jama’a ku taya mu mu kama Safara’u da Mr 442 domin a hukunta su

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
August 28, 2022
in Labarai
0
Safiya Yusuf (Safara'u) da Mubarak Abdulkarim (Mr 442)

Safiya Yusuf (Safara'u) da Mubarak Abdulkarim (Mr 442)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNATIN Jihar Kano ta yi kira ga jama’a da su taimaka mata ta kama fitattun mawaƙan nan biyu da aka fi sani da Safara’u da Mr 442 domin a hukunta su saboda “waƙoƙin baɗala” da su ke yi a soshiyal midiya. 

A shelar da ta yi, gwamnatin ta buƙaci jama’a da su taya ta wajen yi wa matasan biyu kwanton ɓauna a duk lokacin da aka gan su a cikin jihar domin a cafke su a kai su kotu. 

Sunan Safara’u na sosai dai Safiya Yusuf, yayin da shi kuma Mr 442 sunan sa Mubarak Abdulkarim.

Safara’u ta yi fice ne a shirin diramar ‘Kwana Casa’in’ na tashar talbijin ta Arewa24, kuma sunan ta ya ƙara yaɗuwa ne bayan an cire ta daga shirin a cikin shekarar 2020 bayan ɓullar wani bidiyon tsiraici da ta yi.

Shi kuma 442, wanda ɗan Zariya ne, ya fara yin fice ne bayan waƙar zambon da ya yi wa jaruma Maryam Booth kan wani bidiyon ta na tsiraici da kuma tsare shi da ta sa aka ɗan yi.

Safara’u da 442 sun shiga bakin duniya tun lokacin da su ka haɗe waje guda su na yin guntayen bidiyo waɗanda su ke wallafawa a Instagram, masu ɗauke da kalamai da rawar batsa.

Shugaban Hukumar Tace Finafinai Da Ɗab’i ta jihar, Alhaji Isma’il Na’abba (Afakallahu), ya ce abin da su ke yi ya saɓa wa dokar hukumar sa, don haka tilas ne a gurfanar da su a gaban alƙali domin a hora su.

Afakallahu ya bayyana haka ne a lokacin da ya tattauna da mujallar Fim a ofishin sa a jiya Asabar.

Safara’u da 442: ana neman su ruwa a jallo

Ya ce: “Wannan umarnin ba tun yanzu ba ne mu ka baza komar mu ta farautar waɗannan mutane, sai dai yanzu ne da labarin ya fita ake ganin kamar yanzu ne. Amma mun daɗe da sanar da neman su, kuma mun yi hakan ne a sakamakon waƙoƙin batsa da suke saki na ɓata tarbiyyar mutane.

“Ba wai ita hukumar ta na kallon su ne a matsayin mawaƙa ba, sai don abin da su ke yi na batsa da ɓata tarbiyya. Kuma duk abin da za ka yi na neman abinci, idan har akwai saɓa wa Allah a cikin sa, sai dai ka ci guba, ba dai ka ci abinci ba. 

“Kuma idan ka kalla, a yanzu ba sa ma ƙasar, daga can su ke yi su ke turawa a soshiyal midiya. Kuma babu wani uba ko uwa da zai bar ɗan sa ya ci gaba da irin waɗannan abubuwa na ɓarna da sunan ya na tura saƙo.

“Da man saƙo kala biyu ne: akwai na ɓarna, akwai na alkhairi. To, su wannan da su ke turawa na ɓarna ne. Ana yin waƙoƙin ɓarna ana yin batsa waɗanda ba su dace ba.

“Ita kuma hukumar an samar da ita ne saboda yaƙi da irin wannan. Don haka duk wanda ya taka dokar wannan hukumar, mu na mai tabbatar masa da cewa ya haɗiyi taɓarya!

“Don haka jama’a su taya mu wajen kawar da irin waɗannan abubuwan, don aikin nan ba na hukuma ita kaɗai ba ne, na jama’a ne baki ɗaya. Saboda haka babu wanda zai zo garin nan don ya samu ɗaukaka ta shaiɗanci mu bari ya lalata mana tarbiyyar mu ta addini.

“Don haka lallai mu na neman su, kuma mun ba da sanarwar a dukkan gidajen da ake yin wasanni da gidajen da ake yin bukukawa duk irin waɗannan waƙoƙin ba za a saka su ba.”

Shugaban ya ƙara da cewa, “Ita hukuma abin da ya bayyana shi ta ke iya karewa, don ba za ta shiga gidajen mutane ta ga me su ke kallo su da iyalan su ba. Mu abin da ya bayyana shi mu ke hukunci a kan sa, don haka mu ka ce ba za a saka waƙoƙin a gidajen wasanni ko wajen taron biki ba, don haka mu ka kira iyaye da magidanta da su hana abubuwan ta ɓangaren su.

“Don haka, mutane su gane ko su waɗannan da su ka yi laifin ba mu su ka yi wa laifi ba, doka su ka taka, don haka duk lokacin da mu ka kama su za mu tattara ne mu kai su ga hukuma. Kotu ce za ta yi masu hukunci. Don haka ba Afakallahu ne zai zauna ya ce ka yi ba daidai ba a yanke maka hukunci. Don haka lallai za mu gurfanar da su ne a gaban kotu, domin sun karya dokar Jihar Kano da kuma rashin girmama mutanen Jihar Kano.

“Kuma gudun da su ka yi, ya nuna hukumar a tsaye ta ke wajen kare dokoki da jama’ar Kano a kan duk wani abu da zai kawo barazana a gare su. Kuma duk wanda ya ke ganin zai karya doka, to ga shi ga wajen. “

Afakallahu ya yi kira ga iyaye da su sa ido kan tarbiyyar ‘ya’yan su domin zamani ya zo na soshiyal midiya inda akwai ƙalubale a gaban su a kan abin da ya shafi wayoyin ‘ya’yan su. 

Ya ce: “Duk abin da ka ke ganin ka yi na tarbiyya, cikin ƙaramin lokaci za a rusa shi. Don haka ka sa idanu a kan yaran ka. In dare ya yi, duk wata mace a karɓe wayar ta, saboda wasu abubuwan sai kun kwanta ake yin su.”

Loading

Tags: Arewa24baɗalabatsagwamnatin KanoHukumar Tace FinafinaiIsma'il Na'abba AfakallahukotuMaryam BoothmawaƙaMr 442Mubarak AbdulkarimSafiya Yusuftsiraici
Previous Post

Hukumar Hisbah ta goyi bayan manufofin ƙungiyar mata ‘yan fim

Next Post

Rarara ya yi wa zakarun gasar ‘Jagaba Shi Ne Gaba’ ruwan naira da motoci da waya

Related Posts

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa
Labarai

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa

July 17, 2025
Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Next Post
Ɗanhajiya na karɓar motar da ya lashe a matsayin wanda ya zo na ɗaya

Rarara ya yi wa zakarun gasar 'Jagaba Shi Ne Gaba' ruwan naira da motoci da waya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!