• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Saturday, June 7, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Fashewar gas a Kano: Ministar Jinƙai na so a ɗau matakan hana aukuwar bala’o’i

by DAGA ALI KANO
May 18, 2022
in Nijeriya
0
'Yan kallo a bakin ginin da ya ruguje (Hoto daga: NEMA)

'Yan kallo a bakin ginin da ya ruguje (Hoto daga: NEMA)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAR Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta ɗaukar matakan hana aukuwar fashewar abubuwa da kuma rugujewar gine-gine a ƙasar nan.

Ta yi kiran ne sakamakon fashewar silindar iskar gas da ta faru a unguwar Sabon Garin Kano har ta yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama.

Hukumar Gudanar da Aikin Agajin Gaggawa (NEMA), wadda ke ƙarƙashin ma’aikatar ta Sadiya, ta bayyana tun da farko cewa wani gini ya ruguje a sanadiyyar fashewar gas ɗin, kuma an tsamo gawarwakin mutum tara daga cikin bulullukan rusasshen ginin wanda ke daura da inda gas ɗin ya fashe.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa ministar kan aikin jarida ta bayar, wato Nneka Ikem Anibeze, an ruwaito Hajiya Sadiya ta na bayyana alhini kan faruwar lamarin, yayin da kuma ta jajanta wa iyalan waɗanda abin ya shafa da kuma gwamnatin Jihar Kano.

Ministar ta bayyana al’amarin da cewa wani abu ne mai ƙona rai kuma ibtila’i ne, har ta ƙara da cewa: “Wannan abin baƙin ciki ne. Iskar gas ta fashe, gini ya ruguje, kuma mutane da dama da abin ya ritsa da su sun rasu, sannan ana faman ceto wasu daga cikin bululluka da rodin ginin… wannan babban abin baƙin ciki ne.

“Ina jajanta wa iyalan waɗanda su ka rasu da kuma gwamnatin Jihar Kano. 

“Yawaitar aukuwar fashewar abubuwa a ƙasar nan a cikin ‘yan kwanakin nan ta na da ban-tsoro, kuma mu na kira ga hukumomin da su ka kamata da su yi wani abu da sauri don hana ci gaba da aukuwar fashe-fashe da rugujewar gini a ƙasar nan.”

Wata mota a wajen da silindar gas ɗin ta fashe

Darakta-Janar na NEMA, Alhaji Mustapha Habib Ahmed, ya tura motocin haƙar ƙasa kuma ya riƙa bada umarni wajen aikin ceton rai a wajen da abin ya faru tare da haɗin gwiwar hukumar agajin gaggawa ta jihar, wato SEMA, da ƙungiyar agaji ta Red Cross ta Nijeriya, da hukumar ‘yan sanda, da hukumar tsaron lafiyar ƙasa (Civil Defence) da sauran masu kai agaji don tabbatar da an ceto mutanen da ginin ya zube a kan su tare da kai su asibiti don a yi masu magani.

Bayan fashewar gas ɗin dai, an riƙa yaɗa ji-ta-ji-ta a soshiyal midiya cewa wai bam ne ya tashi, har sai da hukumar ‘yan sanda ta ƙaryata labarin.

Kwamishinan ‘Yanda na Jihar Kano, Alhaji Sama’ila Dikko, ya fito ya ce, “Ba bam ba ne ya tashi, silindar gas ce ta fashe. Mun san hakan saboda wani mutum wanda ya na cikin waɗanda abin ya fara ritsawa da su wani mai walda ne a wannan yankin.

“Mutum huɗu sun rasa ran su, waɗanda sun haɗa da maza biyu da mace ɗaya, amma ba mu sami ɗalibi wanda fashewar ta ritsa da shi ba.”

Loading

Tags: agaji da inganta rayuwabuilding collapseCivil Defence CorpsDisaster Management and Social Developmentfashewar gasgas explosionKanoMinistar Harkokin JinƙaiMinistry of Humanitarian AffairsMustapha Habib AhmedNEMANigerian Red CrossNneka Ikem Anibezepolicerugujewar giniSabon GariSadiya Umar Farouq
Previous Post

Ranar Iyalai ta Duniya: Ma’aikatar Jinƙai za ta agaza wa iyalai mabuƙata 30

Next Post

Zan yi amfani da sarautar da aka ba ni wajen inganta rayuwar matasa, inji Fatima Lamaj

Related Posts

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya za ta tallafa wa yekuwar rigakafin cutar ƙyandar Jamus

June 4, 2025
Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London
Nijeriya

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

May 16, 2025
Next Post
Jakadiya, Hajiya Fatima Ahmed Ibrahim (Lamaj), tare da dogari jim kaɗan bayan naɗin ta

Zan yi amfani da sarautar da aka ba ni wajen inganta rayuwar matasa, inji Fatima Lamaj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!