• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Friday, July 18, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Kano ta sake tsare mawaƙi Nazir M. Ahmad

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
November 4, 2020
in Labarai
0
Daga dama: Nazir M. Ahmad da Isma'il Na'abba (Afakallah)

Daga dama: Nazir M. Ahmad da Isma'il Na'abba (Afakallah)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
HUKUMAR Tace Finafinai ta Jihar Kano ta sake kama shahararren mawaƙi Nazir M. Ahmad (Sarkin Waƙa).
 
Ɗan’uwan sa, darakta Aminu Saira, shi ne ya sanar da haka a shafin shi na Instagram, inda ya ce: “Ina mai alhinin sanar da ‘yan’uwa da abokan arziki cewa Hukumar Tace Finafinai, ƙarƙashin Gwamnatin Jihar Kano, ta sake kama ɗan’uwa na, Nazir M. Ahmad (Sarkin Waƙa).
 
“A yanzu haka ya na tsare. Ƙarin bayani na nan tafe.”
 
Mujallar Fim ta ruwaito cewa wannan ba shi ne karo na farko da hukumar ta kama Nazir ba, domin kuwa a shekarar da ta gabata ne ta fara kama shi bisa zargin sakin wani kundin waƙoƙi ba tare da ya je hukumar ta tantance su ba.
 
An gurfanar da shi a kotu, inda daga baya ya samu beli. 
 
Wata majiya ta bayyana wa mujallar Fim cewa wannan kamun da aka yi wa mawaƙin ya na da nasaba da wancan kes ɗin na bara.
 
Majiyar ta ce da ma can a bisa beli ne aka bar Nazir ya na shawagi, to amma kuma wai ya karya ƙa’idar belin, “shi ya sa aka sake kama shi”.
 
Majiyar ta ce hukumar ta fito da sababbin tsauraran ƙa’idojin beli, waɗanda su ka haɗa da tilas ne mawaƙin ya kawo wani babban basarake, kamar wakilin Sarki a gundumar su, ko wani babban darakta a gwamnatin Jihar Kano, domin ya tsaya masa kafin a ba shi sabon beli.
 
Majiyar ta ce, “Samun sabon belin zai ɗan yi wuya domin da yawa a gwamnati da kuma masarauta ana kallon Nazir a matsayin ɗan adawa.”
 
Nazir dai shi ne Sarkin Waƙar Sarkin Kano Alhaji Muhammadu Sanusi II, wanda aka tuɓe kwanan baya.
 
Mujallar Fim ta yi ƙoƙarin jin ta bakin mai magana da yawun hukumar tace finafinan kan wannan sabon salo da shari’ar Nazir ta ɗauka, amma sai ya bayyana mana cewa shi ma bai da masaniya kan kama mawaƙin da aka yi.
 
Haka kuma wakilin mu ya yi ƙoƙarin jin ta bakin shugaban hukumar, Alhaji Isma’ila Na’abba (Afakallah), amma hakan ma ba ta samu ba.

Loading

Previous Post

Cewar Rahama Sadau: Jama’a na tuba, ku yafe ni

Next Post

‘Maimuna Gandama’: Tsakanin tallata al’ada da ɓata tarbiyya

Related Posts

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Next Post
‘Maimuna Gandama’: Tsakanin tallata al’ada da ɓata tarbiyya

'Maimuna Gandama': Tsakanin tallata al'ada da ɓata tarbiyya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!