• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, April 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Tarayya ta jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu a turereniya, ta ba da shawara kan bukukuwan Kirsimeti 

by WAKILIN MU
December 22, 2024
in Nijeriya
0
Gwamnatin Tarayya ta jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu a turereniya, ta ba da shawara kan bukukuwan Kirsimeti 

Alhaji Mohammed Idris

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jajanta wa iyalai da ‘yan’uwan waɗanda suka rasa rayukan su a hatsarin turereniya yayin rabon abinci da aka yi a Ibadan, Abuja, da Okija.

A cikin wata sanarwa da Rabi’u Ibrahim, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai ga Ministan, ya fitar a ranar Lahadi, ya ruwaito Idris yana cewa: “Tunanin mu da addu’o’in mu suna ga waɗanda suka rasa rayukan su da iyalan su da duk wanda wannan mummunan al’amari ya shafa.”

Ministan ya ce waɗannan abubuwan baƙin ciki sun yi matuƙar girgiza gwamnati kuma ya jaddada muhimmancin tabbatar da gudanar da taron jama’a yadda ya kamata yayin gudanar da irin waɗannan ayyukan alheri, musamman a lokacin bukukuwan Kirsimeti.

Duk da yake ya yaba da kyawawan niyyar waɗanda suka shirya irin waɗannan ayyuka domin taimaka wa mabuƙata, ministan ya gargaɗi dukkan mutane da ƙungiyoyi da suke shirin gudanar da irin waɗannan ayyukan da su bi umarnin da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Mista Kayode Egbetokun, ya bayar kan a riƙa tuntuɓar ofisoshin ‘yan sanda domin gudanar da tsari mai kyau na kula da jama’a da tsaro.

Ya jaddada cewa haɗin kai tsakanin jami’an ‘yan sanda da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) yana da matuƙar muhimmanci wajen kare rayuka da tabbatar da cewa irin wannan ƙoƙarin na agajin mabuƙata bai haifar da wata damuwa ba.

Haka kuma Idris ya yi kira ga ‘yan siyasa da sauran masu ruwa da tsaki da su guji siyasantar da irin waɗannan mummunan al’amuran, yana mai bayyana cewa waɗannan munanan al’amura ba su da alaƙa da tada komaɗar tattalin arziki na gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke yi.

“Ya kamata a lura da cewa a baya an taɓa samun aukuwar irin waɗannan abubuwan takaici, kafin zuwan wannan gwamnati mai ci, don haka duk wani yunƙuri na danganta waɗannan bala’o’i da gyare-gyaren Shugaban Ƙasa ba shi da tushe kuma ba gaskiya ba ne,” inji shi.

Idris ya ce gyare-gyaren da ake yi, yayin da suke sake fasalin tattalin arzikin Nijeriya domin samun cigaba mai ɗorewa, an tsara su ne domin inganta rayuwar dukkan ‘yan Nijeriya, musamman mabuƙata, ba tare da haifar da wata damuwa ba.

Ministan ya yi kira ga ‘yan ƙasa da su haɗa kai wajen tabbatar da cewa lokacin bukukuwan Kirsimeti ya kasance lokacin zaman lafiya, kyakkyawan hali, da farin ciki, ba tare da abubuwan baƙin ciki da za a iya kauce wa ba.

Loading

Tags: jajeKirsimetiMohammed Idristurereniya
Previous Post

Zauren Manazartan Makaɗa da Mawaƙan Hausa ya yi taron bikin cika shekara 10 da kafuwa

Next Post

Ƙura ta tashi a MOPPAN: Ana zargin shugaban kwamiti, Bello Achida, da siyasantar da babban zaɓen ƙungiyar

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Ƙura ta tashi a MOPPAN: Ana zargin shugaban kwamiti, Bello Achida, da siyasantar da babban zaɓen ƙungiyar

Ƙura ta tashi a MOPPAN: Ana zargin shugaban kwamiti, Bello Achida, da siyasantar da babban zaɓen ƙungiyar

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!