HUKUMAR Hisbah ta Jihar Kano ta bayyana goyon baya ga manufofin sabuwar ƙungiyar nan ta matan Kannywood mai suna ‘Association of Kannywood Female Artistes’ (AKAFA) tare da yaba wa ayyukan ta.
Yabon ya fito ne daga bakin Babban Kwamandan hukumar, Ustaz Haruna Sani ibn Sina, a lokacin da wata tawagar ƙungiyar ta kai masa ziyara a ofishin hukumar da ke unguwar Sharaɗa a cikin birnin Kano.
A jawabin sa ga maziyartan, Ustaz Ibn Sina ya nuna farin ciki da ziyarar da ƙungiyar ta kai masu tare da cewa manufofin ƙungiyar da yadda su ke tafiyar da su sun yi daidai da ayyukan Hukumar Hisbah na daƙile ayyukan ɓarna, don haka hukumar ta amince da ta bai wa ƙungiyar goyon baya wajen cimma manufofin ta na gyara, domin inganta rayuwar matasa.

Tun da farko da ta ke Jawabi a game da zuwan nasu, sai da Shugabar ƙungiyar ta AKAFA, Hajiya Rashida Abdullahi Maisa’a, ta bayyana cewa sun je hukumar ne domin gabatar da kan su da kuma neman a haɗa hannu a yi aiki tare domin magance matsalar da ke tasowa a cikin ‘yan fim lokaci zuwa lokaci, wanda in aka haɗa ƙarfi, za a samu a yi maganin matsalolin.
Ita ma a nata jawabin, Mataimakiyar Shugaban Hukumar Hisbah a ɓangaren mata, Malama Ummukhulsum Ƙasim, ta yaba wa yunƙurin mata’ yan fim na kafa ƙungiyar da su ka yi da kuma tunanin su na tsaftace sana’ar su tare da yaba masu wajen kyautata mu’amala da kamun kai.
Shi ma mai ba Gwamna shawara a kan hukumar ta Hisbah, Alhaji Mujittaba Baban Usama, ya yi masu fatan alheri tare da kira a gare su da su tsarkake niyya a wajen gudanar da aikin nasu yadda za a samu a inganta tarbiyyar al’ummar Musulmi.
Tun dai bayan kafa ƙungiyar a watan Yuli da ya gabata, shugabannin ta su ka tashi tsaye domin zagayawa da kai ziyara ga manyan mutane da hukumomi a Jihar Kano domin gabatar da ƙungiyar da kuma neman goyon bayan su a game da aikin da ƙungiyar ta sa a gaba na tsaftace masana’antar shirya finafinan Hausa.

