HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta aika wa Fadar Shugaban Ƙasa da wasiƙar da batutuwan da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe ya ƙunsa.
Sai dai kuma hikumar ta shawarci Shugaba Muhammadu Buhari da ya tuntuɓi jam’iyyun siyasa da ɓangarorin jami’an tsaro dangane da ƙudirin da aka shigar cewa zaɓen ‘yar-tinƙi jam’iyyu za su riƙa yi a wurin zaɓen fidda-gwanin ‘yan takara.
A ranar 29 ga Nuwamba ne Majalisar Dattawa ta aika wa Buhari Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe, wanda shi kuma a bisa doka ya na da kwana 30 kacal da zai ɗauka ya sa wa ƙudirin hannu domin ya tabbata doka kenan.
Shi dai wannan sabon ƙudiri, matsawar Buhari ya sa masa hannu, to ya shafe Dokar Zaɓe ta 2010 kenan, wadda ita ce aka yi wa kwaskwarima.
A cikin kwaskwarimar an nemi a riƙa yin zaɓen ‘yar-tinƙi wajen fitar da ‘yan takara.
Sai kuma batun aika sakamakon zaɓe ta yanar gizo da sauran na’urori da kafafen sadarwa na zamani.
Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Fargesa Ibrahim Gambari, shi ne ya rubuta wa INEC wasiƙa, inda ya nemi hukumar ta rubuto shawarwari ga Buhari kan batutuwan da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe su ka ƙunsa.
Gambari ya shaida wa INEC cewa kada shawarwarin su wuce ranar 3 ga Disamba.
Batun a koma yin zaɓen ‘yar-tinƙi wajen zaɓuɓɓuka na fidda-gwanin takarar jam’iyyu ya haifar da ka-ce-na-ce a cikin jam’iyyar APC mai mulki. Yayin da ‘yan majalisa waɗanda mafi rinjaye ‘yan APC ne, su da ɓangaren Bola Tinubu ke goyon bayan ‘yar-tinƙe, su kuma yawancin gwamnoni sun fi so a bar tsarin yadda ya ke, wato wakilai su riƙa yin zaɓen fidda-gwani tun daga mazaɓu har zuwa sama.