• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, April 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

INEC za ta fara sabon aikin rajistar masu zaɓe a farkon 2021

by DAGA WAKILIN MU
November 5, 2020
in Nijeriya
0
Farfesa Mahmood Yakubu a gaban 'yan jarida a wani lokaci can baya. Hoto: NAN

Farfesa Mahmood Yakubu a gaban 'yan jarida a wani lokaci can baya. Hoto: NAN

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce za ta soma wani sabon aikin yi wa masu zaɓe rajista a cikin watanni uku na farko na shekarar  2021.
 
Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka ga manema labarai a Abuja a ranar Laraba bayan ya bayyana a gaban Kwamitin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa na Majalisar Dattawa domin ya kare kasafin kuɗin hukumar na shekarar 2021.
 
A cewar sa, za a yi aikin yin rajista har zuwa watanni shida kafin a yi manyan zaɓuɓɓukan shekarar 2023.
 
Ya ce, “Za mu ci gaba da gudanar da aikin yin rajistar masu zaɓe a watanni uku na farkon shekarar 2021. Kuma da zarar mun ci gaba, aikin zai ci gaba babu tsayawa har zuwa shekara ɗaya da rabi, aƙalla watanni shida kafin a yi manyan zaɓuɓɓukan da ke gaba.”
 
Haka kuma ya bayyana cewa a yanzu haka hukumar ta na fafatawa a ƙararraki kamar 1,700 na kafin zaɓe da bayan zaɓe da aka kai kotu daga zaɓuɓɓukan shekarar 2019.
 
Sai dai kuma ya ce hukumar ba ta biyan lauyoyi manyan kuɗaɗen shari’un da ake yi amma ta na dai biyan kuɗaɗen da Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya ta ƙayyade.
 
Farfesa ya ce, “Misali, idan mu na da shari’a daga zaɓen gwamna a Kotun Ƙoli, kuɗi mafi yawa da za mu biya lauyoyi shi ne naira miliyan 4.5, amma saboda yawan shari’un mun kusa samun ƙararraki har guda 1,700 na kafin zaɓe da na bayan zaɓen shekarar 2019 kaɗai.
 
“A ko yaushe za ka ji mutane su na zuwa kotu tare da haɗa INEC a ƙarar su, amma mu dai za mu ci gaba da yin abin da za mu iya ne da iyakar abin da ke aljihun mu.”
 
Tun da farko a jawabin sa ga Majalisar Dattawan, Farfesa Yakubu ya ce hukumar ta tsara za ta ɗauko kuɗi naira biliyan 5.2 daga asusun ta na naira biliyan 10 ta haɗa cikin kasafin ta na shekarar 2020.
 
Ya ce hukumar ba ta taɓa kashe ko kwabo ba daga wannan asusun tun da aka kafa ta a cikin 2010, yayin da ya ce dalilin da zai sa a ciro kuɗin shi ne saboda rage mata kuɗi da aka yi a kasafin shekarar 2020.
 
Ya ce, “Abin da ya faru yanzu shi ne kasafin mu na shekarar 2020 ya yi ƙasa da naira biliyan 40 daga naira biliyan 45.5 a shekarar 2019.
 
“Saboda kashi 10 cikin ɗari na kuɗin da aka zabtare saboda annobar korona, sai kuma kuɗin su ka ƙara raguwa zuwa naira biliyan 36 a tsakiyar shekarar a lokacin da mun riga mun gama shirye-shiryen kashe kuɗaɗen.
 
“Saboda haka, tunda dai an yi asusun ne saboda lokaci irin na yau da ake buƙatar sa, na sanar da kwamitin cewa ranar buƙatar kuɗin ta zo.
 
“Don haka, za mu ciri wani sashe na kuɗin asusun domin mu yi balas da kasafin mu na bana.”
 
A kan batun bai wa ‘yan Nijeriya mazauna ƙasar waje damar yin zaɓe a inda su ke, shugaban ya ce hakika hukumar ta na son ganin ta ba su dama su yi zaɓe, amma tabbatar da yiwuwar hakan ya na buƙatar a yi wa tsarin mulki da kuma Dokar Zaɓe garambawul.
 
Ya ce, “Mun riga mun gama tsara takardun, da zarar an gyara dokar, to za mu iya fara aiwatarwa.
 
“Mun gama shiri, mun yi zama da dama da su ‘yan Nijeriya a Hukumar Mazauna Ƙetare, wato Diaspora Commission (NIDCOM), amma ba za mu iya tsallake abin da doka ta tanadar ba.”

Loading

Previous Post

‘Maimuna Gandama’: Tsakanin tallata al’ada da ɓata tarbiyya

Next Post

Yadda Sufeto-Janar ya umarci kwamishina ya kama Rahama Sadau

Related Posts

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa
Nijeriya

Yadda CBN ke tallabe da tattalin arzikin Nijeriya, yayin sa farashin ɗanyen mai ke faɗuwar-‘yan-bori a kasuwa

November 7, 2025
Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji
Nijeriya

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

November 2, 2025
Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba
Nijeriya

Bankin CBN ya yunƙuro: Naira ta hana dala numfashi mai ƙarfi a ƙarshen Oktoba

November 2, 2025
Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje
Nijeriya

Bankin CBN ya ƙaryata ƙazafin sayar wa manyan dillalan mai dala biliyan 1.259 domin su shigo da fetur daga waje

October 29, 2025
Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Nijeriya

Tinubu ya yi adalci ga dukkan yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

August 31, 2025
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Next Post
Rahama (daga hagu) da ƙannen ta: Zainab, Aisha da Fatima

Yadda Sufeto-Janar ya umarci kwamishina ya kama Rahama Sadau

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!