• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, June 4, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Jan Hankalin ‘Yan Arewa Kan Yin Abin Da Ya Dace

by DAGA ABDULHADI MUHAMMAD SANI
December 13, 2021
in Mawaƙa
0
Malam Abdulhamid Muhammad Sani (Malumma Matazu)

Malam Abdulhamid Muhammad Sani (Malumma Matazu)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

(Sadaukarwa ga Hajiya Rahma Abdulmajid,
Hajiya Zahra’u Usman
da Hajiya Bint Hijazi)

“Mu haɗa kai ‘yan Arewa mu yi abin da ya dace”

1. Bismillah da Sunan Allah Rabbana  Mahalicce.

2. Mahaliccin duk ‘yan’adam, bishiya da itace.

3. Kai ka ɗaukaka mu bil’adam duk mazan mu da mace.

4. Kan na fara salati na yi ga Shugaba mafifice.

4. Shumagaban mu Rasulullah mai kyau a siffa da zance.

5. Na sa iyali nai Ahlulbait masu kyawun kwatance.

6. Sannan Sahabban Nabiyullah nagargartu kun yi dace.

7. Nai yekuwa ‘yan Arewar mu mu yi abin da ya dace.

8. An kashe mu a hanya har a gidan mu ma an yi ƙwace.

9. Ana ta fyaɗe ga mata, shanayen mu ma an ka kwance.

10. An sa rashin jituwa tsakankanin mu Hausa-Filance.

11. Ana ta yin garkuwa da mu ‘ya’yan mu har ‘ya mace.

12. Sannan mu bada kuɗin fansa yankin mu mun fa kurumce.

13. Mu na ta ƙara masu ƙarfi Arewa mun fa makance.

14. Zaɓaɓɓun mahukunta sun ƙi abin da ya dace.

15. Muggan makamai sun yayyaɗu Arewa yau babu zance.

16. Mu haɗa kai ‘yan Arewa mui abin da ya dace.

17. Mu ƙara komawa ga Allah Shi kaɗai mu kaɗaice.

18. Mu ninka istigfarin mu da hailala mu karance.

19.  Sannan mu lizimci Ƙur’ani mu daina duk cece-kucce.

20. Ƙunutu ma mu lizimce ta yin gaskiya ma mu nace.

 21. Mu nemi haƙƙoƙin mu amma cikin shari’ance.

22. Haƙƙin mu ne jerin-gwano cikin abin da ya dace.

23. Har yin zaman dirshan ma mu yi dai abin shari’ance.

24. Duk don mu ja hankulan mahukunta sui abin da ya dace.

25. Mu haɗa kai ‘yan Arewa mu yi abin da ya dace.

26. Abdulhamidi Matazu waƙar ni na yo kar ku mance.

27.  A ‘two thousand twenty-one’ da mun ka zam a ɗimauce.

28. Ran sha biyu ga watan sha biyu amma a miladiyance.

29. Don shajja’a ‘yan Arewa ta mu tashi mu daina kwance.

30. Ya ikhwani liƙa’ul-khair Allah ya sa mun ji zance.

Alhamdu lillah!

  • Abdulhamid Muhammad Sani
    (Malumma Matazu) shi ne shugaban riƙo na
    Gamayyar Marubuta da Manazarta Waƙoƙin Hausa na Nijeriya, reshen Jihar Katsina
    GSM: 08037868097

Loading

Tags: Arewainsecuritymawaƙarashin tsaro
Previous Post

Tarihin Fulani: Mahangai huɗu

Next Post

Mawaƙa mu dawo hayyacin mu

Related Posts

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi
Mawaƙa

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi

April 19, 2025
Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala

October 28, 2024
Abin da ya sa na koma yin waƙa da kayan kiɗan gargajiya – Aminu Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa na koma yin waƙa da kayan kiɗan gargajiya – Aminu Ala

July 16, 2024
Nazarin waƙar ‘Fatima Mai Zogale’ ta Dauda Kahutu Rarara
Mawaƙa

Nazarin waƙar ‘Fatima Mai Zogale’ ta Dauda Kahutu Rarara

May 13, 2024
Waɗansu waliyyai a Nijar da Nijeriya 
Mawaƙa

Waɗansu waliyyai a Nijar da Nijeriya 

December 7, 2023
Ɗaliban Hausa ‘yan ƙasar Sin sun ziyarci mawaƙi Aminu Ala
Mawaƙa

Ɗaliban Hausa ‘yan ƙasar Sin sun ziyarci mawaƙi Aminu Ala

December 3, 2023
Next Post
'Yan ta'adda irin waɗanda su ka addabi arewacin Nijeriya

Mawaƙa mu dawo hayyacin mu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!