• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, July 23, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Jarumar Kannywood Rashida Maisa’a ta ja kunnen Ganduje: Haramcin A Daidaita Sahu zai hana APC cin zaɓe a Kano

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
November 30, 2022
in Labarai
0
Rashida Adamu Abdullahi (Maisa'a) ta na jan kunnen Ganduje cikin bidiyon da ta yi

Rashida Adamu Abdullahi (Maisa'a) ta na jan kunnen Ganduje cikin bidiyon da ta yi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

JARUMA, babbar furodusa a Kannywood kuma ‘yar siyasa a Kano, Rashida Adamu Abdullahi (Maisa’a), ta yi nuni da cewa idan har gwamnatin Kano ba ta soke dokar hana baburan A Daidaita Sahu bin wasu tituna a Kano ba, to da wuta jam’iyyar APC ta ci zaɓe a jihar da ma Nijeriya ba ki ɗaya.

Jarumar bayyana takaicin ta dangane da dokar ta gwamnatin wadda ta fara aiki ne daga yau Laraba, 30 ga Nuwamba, 2022.

Rashida dai ƙusa ce a tafiyar gwamnatin Dakta Abdullahi Umar Ganduje, inda har an ba ta muƙamin mai ba gwamna shawara.

Jarumar ta saki wani guntayen bidiyo guda uku a soshiyal midiya, musamman TikTok da Instagram, inda ta bayyana alhinin ta kan sabuwar dokar.

A bidiyon farko, wanda a kan sa ta rubuta, “Wannan wace irin masifa ce,” furodusar ta ce: “In dai ana so APC ta ci zaɓe a Jahar Kano, wallahi maganar A Daidaita Sahu a janye ta.

“An ce ‘yan A Daidaita Sahu su rinƙa tashi daga ƙarfe goma. Baba, sun ɗauki wannan maganar da aka gaya masu.

A bidiyo na biyu, Rashida ta ce ta faɗi gaskiya ko da za a tsire ta ne

“Zaɓe ya ƙarato, idan mu ka rasa ‘yan A Daidaita Sahu a Kano wallahi mun shiga uku. A taimaka wa Dakta Nasiru Yusuf Gawuna. In dai ana son ya ci gwamnan nan a Jahar Kano, da shi da Murtala Sulen Garo, a janye maganar A Daidaita Sahu don girman zatin Allah, Baba Ganduje.

“Ba mu ɗauko hanyar cin zaɓe ba! Ba mu ɗauko hanyar cin zaɓe ba! Duk wanda ya faɗi wannan maganar ‘yan A Daidaita Sahu, wallahi ba ya so mu ci zaɓe a Jihar Kano.”

A bidiyo na biyu da ta yi, Rashida ta bayyana cewa su magoya bayan APC su na faɗi-tashi a kullum don ganin an samu nasara, amma sai gwamnati ta riƙa zuwa ta na aikata abin da bai dace ba.

Ta ce to ita dai ba za ta yi shiru ba a game da wannan dokar, ya zama dole ta yi magana ko da kuwa a za tsire ta.

A bidiyo na uku, wanda akwai alamar ya na da alaƙa da sauran biyun, an ga jarumar ta na tafiya a mota ta na jin waƙar Ali Jita inda ya ke faɗin: “Allah sarki duniya, idan wani ya ƙi ka wani ya bar ka, wani zai so ka!”

Loading

Tags: A Daidaita SahuAbdullahi Umar GandujeAPCharamciKanoMurtala Sulen GaroNasiru Yusuf GawunaRashida Adamu Abdullahi Maisa'aZaɓen 2023
Previous Post

Shekara 10 da aure: Ina alfahari da zama na da Sumayya, inji Jamilu Ibrahim

Next Post

Hare-hare: Shugaban INEC ya lissafa asarar da aka yi, da hanyoyin samun mafita

Related Posts

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa
Labarai

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa

July 17, 2025
Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Next Post
Farfesa Mahmood Yakubu ya na jawabi a taron

Hare-hare: Shugaban INEC ya lissafa asarar da aka yi, da hanyoyin samun mafita

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!