• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, July 23, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Kotu ta bada odar tsare Murja Kunya a kurkuku tsawon kwana tara

by MUKHTAR YAKUBU
February 14, 2024
in Labarai
0
Kotu ta bada odar tsare Murja Kunya a kurkuku tsawon kwana tara

Murja Ibrahim Kunya

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A JIYA Talata aka tura shahararriyar ‘yar Tiktok ɗin nan Murja Ibrahim Kunya gidan yari a Kano a bisa umurnin kotu.

Kotun Shari’ar Musulunci da ke zaman ta a unguwar Gama PRP, Kano, ta ce a tsare ta ne bisa tuhumar da Hukumar Hisbah ta shigar inda ta zarge ta da aikata laifuffukan da suka haɗa da kawo ɓata-gari cikin dare, aikata baɗala, tada hatsaniya da kuma razanarwa.

Laifuffukan sun saɓa wa sashe na 341, 275 da 227 na kundin finalkod.

Tun da farko dai, jami’an Hukumar Hisbah sun cafke Murja bayan wasan ɓuya da suka yi da ita a sakamakon shelar neman ta da suka yi, sakamakon wasu ƙorafe-ƙorafe da wasu mazauna unguwar Tishama a Kano inda Murja ɗin take da zama suka yi kai wa Hisbah.

A kotun, an karanta wa Murja tuhumar zargin, ita kuma ta musanta dukkan tuhumar da ake yi mata.

Lauyan da ke kare ta, Barista Aliyu Umar, ya roƙi kotun da ta bayar da belin ta, dogaro da sashe na 35 da 36 na dokokin ƙasa, da kuma sashe na 168, 172 da 173 na finalkod.

‘’A sanya ta a hannun beli saboda hurumi ne na kotun, sannan idan ta bayar da belin ta ba za ta gudu ba ko aikata wani laifi da ya saɓa da doka,” inji shi.

Lauyan gwamnati da ya wakilci Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano, Barista Aminu Umar, bai yi suka a kan roƙon lauyan wadda ake tuhumar ba.

Ya ce, “Ba mu da suka a kan wannan roƙo domin bayar da beli hurumin kotu ne,’’ inji shi.

Sai Mai shari’a Malam Nura Yusuf Ahmed, ya bayar da umarnin ci gaba da tsare wadda ake zargin a kurkuku har zuwa ranar 22 ga Fabrairu domin ci gaba da shari’ar.

Wannan dai shi ne karo na biyu da Hukumar Hisbah ta gurfanar da Murja a gaban ƙuliya, domin ko a shekarar da ta gabata ma sai da ta gurfana a gaban kotu inda a wancan lokacin har aka yanke mata hukuncin zaman gidan yari tare da horo na aikin yin sharar masallaci.

Loading

Tags: Hukumar HisbahkotukurkukuMurja Ibrahim KunyaTikTok
Previous Post

Gaskiyar abin da ya faru gare ni a haɗarin da na yi – Jarumar Kannywood Maryam CTV

Next Post

Gwamnatin Tinubu ga gwamnonin PDP: Matsalar Nijeriya ba ta kai ta Venezuela ba

Related Posts

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa
Labarai

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa

July 17, 2025
Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Next Post
Shugaba Bola Ahmed Tinubu

Gwamnatin Tinubu ga gwamnonin PDP: Matsalar Nijeriya ba ta kai ta Venezuela ba

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!