• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Saturday, May 31, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Minista ya sha alwashin ba ‘yan jaridun soshiyal midiya horo kan hanyoyin yaɗa labarai na zamani

by WAKILIN MU
April 18, 2025
in Nijeriya
0
Minista ya sha alwashin ba ‘yan jaridun soshiyal midiya horo kan hanyoyin yaɗa labarai na zamani

Minista Alhaji Mohammed Idris yana jawabi ga 'yan jaridun soshiyal midiya a taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kan jama’a, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada cewa ma’aikatar sa za ta riƙa horas da ‘yan jaridun soshiyal midiya kan hanyoyin watsa labarai na zamani.

Ministan ya faɗi haka ne a cikin saƙon godiya da ya aika wa ‘yan jaridun soshiyal midiya na arewacin ƙasar nan da suka halarci taron farko da ya yi da su a ranar Laraba a Abuja.

A saƙon da ya miƙa musu a bayan taron, ta hannun Daraktan Hulɗa da Jama’a da Tsare-tsaren Baƙi a Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, wato Dakata Suleiman Haruna, ministan ya bayyana farin ciki kan nasarar da aka samu a taron.

A cewar sa, an yi musanyar ra’ayoyi tare da zurfin shawarwari a taron.

Ministan ya ce: “Na ji daɗi sosai kan yadda kuka fayyace tunanin ku tare da faɗin maganganun rungumar kowa a taron.

“Muna sa ran cewa nan gaba za a sake yin irin wannan zaman kafin ƙarshen wannan shekarar.

“Bugu da ƙari, muna da burin faɗaɗa taron ta yadda za a ƙara yawan mamallakan kafafen watsa labarai na soshiyal midiya a tarurruka irin wannan da za a yi a nan gaba.”

Idris yana jawabi ga mahalartan taron

Alhaji Idris ya kuma bayyana cewa daga lokaci zuwa lokaci za a riƙa ɗaukar wasu daga cikin masu halartar taron domin a ba su horaswa ta musamman kan hanyoyin yaɗa labarai da ƙirƙirarrar fasaha (artificial intelligence) wadda Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Tarayya za ta riƙa shiryawa.

Haka kuma ya ce wannan taro da aka yi da ‘yan jaridun soshiyal midiya na Arewa, za a riƙa yin irin sa da takwarorin su na kudancin Nijeriya.

Wani sashe na ‘yan jarida a taron
Minista yana amsa tambayoyin mahalartan taron
An ɗauki hotuna bayan taron

Loading

Tags: Mohammed Idrissoshiyal midiya
Previous Post

Minista ya sake jaddada ƙudirin sabunta kayan aikin watsa labarai na gwamnati

Next Post

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi

Related Posts

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150
Nijeriya

Tinubu ya tura wakilai zuwa Neja kan ambaliyar Mokwa da ta halaka sama da mutum 150

May 31, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta goyi bayan amfani da Ƙirƙirarrar Basira cikin ɗa’a a aikin jarida – Idris
Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a ambaliyar garin Mokwa

May 30, 2025
Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris
Nijeriya

Babu wasu masu juya Tinubu ta bayan fage – Idris

May 25, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris
Nijeriya

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Idris

May 20, 2025
Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London
Nijeriya

Idris ya ƙaryata ji-ta-ji-tar an mayar da taron bayanin ministoci zuwa London

May 16, 2025
Tinubu ya yaba wa Sule Lamiɗo a taron ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar sa
Nijeriya

Tinubu ya yaba wa Sule Lamiɗo a taron ƙaddamar da littafin tarihin rayuwar sa

May 13, 2025
Next Post
Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!