MINISTAN Yaɗa Labarai da Wayar da Kan jama’a, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada cewa ma’aikatar sa za ta riƙa horas da ‘yan jaridun soshiyal midiya kan hanyoyin watsa labarai na zamani.
Ministan ya faɗi haka ne a cikin saƙon godiya da ya aika wa ‘yan jaridun soshiyal midiya na arewacin ƙasar nan da suka halarci taron farko da ya yi da su a ranar Laraba a Abuja.
A saƙon da ya miƙa musu a bayan taron, ta hannun Daraktan Hulɗa da Jama’a da Tsare-tsaren Baƙi a Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, wato Dakata Suleiman Haruna, ministan ya bayyana farin ciki kan nasarar da aka samu a taron.
A cewar sa, an yi musanyar ra’ayoyi tare da zurfin shawarwari a taron.
Ministan ya ce: “Na ji daɗi sosai kan yadda kuka fayyace tunanin ku tare da faɗin maganganun rungumar kowa a taron.
“Muna sa ran cewa nan gaba za a sake yin irin wannan zaman kafin ƙarshen wannan shekarar.
“Bugu da ƙari, muna da burin faɗaɗa taron ta yadda za a ƙara yawan mamallakan kafafen watsa labarai na soshiyal midiya a tarurruka irin wannan da za a yi a nan gaba.”

Alhaji Idris ya kuma bayyana cewa daga lokaci zuwa lokaci za a riƙa ɗaukar wasu daga cikin masu halartar taron domin a ba su horaswa ta musamman kan hanyoyin yaɗa labarai da ƙirƙirarrar fasaha (artificial intelligence) wadda Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Tarayya za ta riƙa shiryawa.
Haka kuma ya ce wannan taro da aka yi da ‘yan jaridun soshiyal midiya na Arewa, za a riƙa yin irin sa da takwarorin su na kudancin Nijeriya.


